ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfani Ya Maka Bankin Globus A Kotu A Kan Karya Yarjejeniyar Bashi

by Bello Hamza
2 years ago
Kamfani

Wani kamfani mai suna ‘Haril Global Solutions Limited’ ya bukaci Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ya umarci Bankin Globus ya biya shi Naira biliyan 10 a kan karya yarjejniyar bashi da suka yi tsakaninsu.

A takardar sammacin karar mai lamba CB/1456/2024, kamfanin ya yi bayanin cewa, bankin ya cire masa wasu kudade daga asusun ajiyarsa ba tare da izinin su ba, wanda hakan ya karya ka’ida da sharuddodin da aka cimma wajen bayar da bashin tun da farko.

  • Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji
  • Gwamnatin Tinubu Na Ƙoƙarin Gyara Kurakuran Baya, Ba Jawo Wahala Ba – Minista

Lauyan kamfanin, Pelumi Olajengbesi Esk., ya bayyana cewa, duk da karya yarjejeniyar kwangilar, sai kuma gashi bankin ya rubuta wa wasu bankuna wasika yana bata sunan kamfaninmu, bankunan da ya rubutawa takardar bantanci sun hada da Access Bank, Fidelity Bank, da kuma Wema Bank.

ADVERTISEMENT

A kan haka ne wadannan bankunan suka bayar da umanin dakatar da amfani da asusun ajiyar kamfanin a bankunan su.

A takardar rantsuwa da wani babban daraktan kamfanin mai suna Oluwaseun Onobun ya sanya wa hannu, ya yi bayanin cewa, a ranar 7 ga watan Disamba na shekarar 2021, bankin Globus ya aiko musu da wasikar amincewa da basu bashin N500,000,000.00 don kamfaninmu ya tayar da komatsar jarin mu da ya yi kasa, an kuma shirya biyan kudaden a cikin shekara daya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Ya ce, wasikar ya samu sa hannun dukkan jami’an bankin, wanda ke nuna amincewa daga Bankin Globus.

Daga nan ya kuma bayyana cewa, cikin ka’idar bashin akwai cewa, za a cire ruwan kashi 16 a cikin dari, za kuma a fra cire kudin bashin ne bayan akalla wata 2 da karbar bashin.

A kan wannan karya yarjejeniyar ne kamfanin ya nemi kotu ta bai wa bankin umarnin biyan diyyar Naira miliyan10 tare da kuma tilasatawa bakin biyan miliyoyin naira da suka cire daga asusun ajiyar kamfanin ba tare da ka’ida ba.

A martaninsu, Bankin ya karyata dukkan ikirarin da kamfanin ya yi, a jawabinsa, lauyan bankin, Tamunosiki Wakama ya nemi kotun ta yi watsi da dukkan bukatun da bankin ta gabatar domin basu da muhimmanci.

Daga karshe kotun ta daga sauraron karar zuwa ranakun 13 da 14 na watan Janairun shekarar 2025.

Kamfani
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Sin Ta Fitar Da Manhajar Na’ura Mai Kwakwalwa Mai Hade Da Fasahar AI Kirar Kasar

Sin Ta Fitar Da Manhajar Na'ura Mai Kwakwalwa Mai Hade Da Fasahar AI Kirar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.