• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar NOUN Za Ta Bai Wa Hafsatu Abdulwaheed Da Innocent Chukwuma Digirin Girmamawa

NOUN Za ta yaye ɗalibai 22,175

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Jami’ar NOUN Za Ta Bai Wa Hafsatu Abdulwaheed Da Innocent Chukwuma Digirin Girmamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar NOUN za ta bayar da digirin girmamawa na dakta ga wasu hamshaƙan ‘yan Nijeriya biyu, wato Hajiya Hafsatu M.A. Abdulwaheed da Cif Innocent Chukwuma, a ranar Asabar 13 Ga Afrilun 2024.

Mataimakin Shugaban jami’ar, Farfesa Olufemi A. Peters, shi ne ya bayyana haka a wajen taron manema labarai da ya yi a Abuja a ranar Litinin kan bikin yaye ɗalibai karo na 13 da jami’ar za ta gudanar a ranar Asabar mai zuwa.

  • Kwamishinar Kidaya Ta Sadaukar Da Albashinta Na Shekara Don Karfafa Mata A Kaduna
  • Maganar Da Aka Taba Fada Min ‘Duk Marubuta ‘Yan Wuta Ne’ Ta Tsaya Min A Rai – Rukayya

Daraktan Yaɗa Labarai na jami’ar, Malam Ibrahim Sheme, ya faɗa a cikin takarda ga manema labarai cewa, ita dai Hajiya Hafsatu Abdulwaheed, ita ce mace ta farko a Arewacin Nijeriya da ta wallafa littafin hikaya, sannan sananniyar ‘yar gwagwarmaya ce mai rajin tallafa wa al’umma.

Littafinta, So Aljannar Duniya, an wallafa shi ne a cikin shekarar 1974.

Shi kuma Cif Chukwuma, shahararren ɗan kasuwa ne wanda ya assasa Innoson Motors, wanda shi ne kamfanin harhaɗa motoci na farko na ‘yan ƙasa da aka kafa a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

A taron manema labaran, Farfesa Peters ya ce, za a ba Hajiya Hafsatu Abdulwaheed digirin girmamawa na Daktar Wallafa ne (wato Doctor of Letters, honoris causa).

 

Ya ce: “Ta sadaukar da rayuwar ta ga hidimar haɓaka harkar ilimi, musamman na ‘ya’ya mata, bisa amanna da cewa, iya karatu da rubutu yana da ƙarfin sauya matsayin al’umma tare da karya lagon fatara da yunwa.”

Shi kuma Shugaban kamfanin Innoson Motors za a ba shi digirin ne a fannin Gudanarwar Kasuwanci (Business Administration) saboda ya ciri tuta a fagen “ƙirƙira, assasawa, tare da sadaukarwa ga amfani da kayan aiki na cikin gida.”

Ya ƙara da cewa ayyukan waɗannan mutane biyu da za a karrama “sun yi daidai da ainihin burukan NOUN na asali na haɓaka ilimin kasuwanci, samar da ababen ilimi, da kuma ƙirƙira.”

Jagoran jami’ar ya yi nuni da cewa NOUN ba ta cika bayar da digirin girmamawa ba, domin na ƙarshe da ta bayar tun cikin 1995 ne, saboda haka sai da ta yi zurfin tunani kafin ta yanke irin wannan shawarar.

Peters ya ce wannan girmamawar da za ta yi babbar nasara ce ga al’ummar jami’ar kuma hanya ce da za a samar da kyakkyawan haɗin gwiwa da ya ginu kan harkar ilimi.

Haka kuma jagoran ya bayyana cewa a bikin na bana jami’ar za ta yaye ɗalibai 22,175 waɗanda daga cikin su guda 15,768 masu digirin farko ne daga tsangayu takwas na jami’ar, sai 6,407 masu digiri na biyu, da ɗalibai shida masu digiri na uku.

Kafin ranar Asabar da za a yi bikin, za a ƙaddamar da sabon Shugaban Jami’a, wato Oba na Benin, Oba Ewuare II, a ranar Alhamis, kuma za a yi taron laccar yaye ɗalibai wadda Mataimakin Shugaban Buɗaɗɗiyar Jami’ar ƙasar Tanzaniya, Farfesa Elifas Bisanda, zai gabatar a ranar Juma’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah ya yi wa Jaruma Saratu Giɗaɗo (Daso) Rasuwa

Next Post

Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.