ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maganar Da Aka Taba Fada Min ‘Duk Marubuta ‘Yan Wuta Ne’ Ta Tsaya Min A Rai – Rukayya

by Leadership Hausa
2 years ago
Rukayya

A makon da ya gabata, mun fara kawo muku tattaunawa da marubuciya RUKAYYA IBRAHIM LAWAN, inda ta bayyana wa masu karatu irin kalubalen da ta fuskanta bayan fara rubutunta. To a wannan makon ma ta zayyano wasu abubuwan ciki har da magana mai daci da aka taba fada mata. Ga karashen tattaunawar tare da wakiliyarmu PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?
Zuwa yanzu dai wata Duniya ne ya fi ba ni wahala wurin rubuta shi kasancewar shi labarin gasa ne, gasar da take da dokoki da ka’idoji. Abin da ya sa ya fi ba ni wahala shi ne bincike, da zaben kalmomi. Kusan kowacce gaba ta labarin bincike ne ya gina ta ga shi rubutu ne da aka kirkire shi a dan takaitaccen lokaci.

Shin kin taba buga littafi?
Eh, na buga guda biyu Gidan Duhu da Wata Duniya. Ina saka ran buga wasu a gaba idan mai duka ya ara mini dama. Da a kwai gajerun labaraina da aka buga a littafan hadaka. Misali; ina da gajeren labari mai taken KASATA a Littafin Dukan Ruwa Ba ya hana Gwarje Amo na hadakar (daliban makarantar Hausa 2021) sai gajeren labari mai taken Wutar Kaiƙayi a littafin Daukar Jinka na hadakar (marubutan da labaransu suka yi zarra a gasar Dangiwa literary 2022).

ADVERTISEMENT

Wane irin nasarori ki ka samu game da rubutu?
Nasarori kam sai dai na ce Alhamdulillah. Nasarar farko da na samu ita ce haduwa da mutanen da ko a mafarki ban yi zaton layin kaddarata zai sada ni fuska da fuska da su ba.

Sai nasarori bangaren gasa. A shekarar 2020 na yi nasar zuwa ta uku a gasar da kunyar jarumai writers ta saka. A 2021 na yi nasarar samun kai wa zagaye biyun karshe na gasar Majalisar marubuta. Duk dai a wannan shekarar labarina ya yi nasarar shiga cikin jerin labarai 25 da BBC suka fara fitarwa na gasar Hikayata. Na san wasu za su iya kallon hakan a ba nasara ba, amma a wurina nasara ce babba zuwa wannan matakin a shekarar farko da na jarraba shiga gasar. Sai shekarar 2022 na yi nasar karbar shaidar girmama daga hannun mai girma gwamnan jihar Katsina a taron gasar Dangiwa literary ta wannan shekarar.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Har ila yau a shekarar 2022 din na samu takardar girmamawa a zagayen kusa da karshe na gasar Aliyu Muhammad research Library (Gusau Institute). Ban fasa gwadawa ba, a shekarar 2023 na yi nasarar lashe kambun girmama (award) na 2 a gasar ta Gusau Institute. Duka dai a 2023 na samu certificate na shida (6th p) a gasar Hazaka writers Association. Wadannan kadan kenan daga cikin nasarorin dana samu silar rubutu.

 

Ya batun kalubale, shin akwai ko babu?

Akwai kalubalai da na fuskanta ga mutane lokacin da na fara rubutu, amma wanda ya fi tsaya mini a rai shi ne wanda aka ce mini duk marubuta ‘yanwuta ne. Sai kuma masu kallon marubuta a matsayin marasa aikin yi. A bangaren masu karatu kuwa kalubalen bai wuce wanda ke addabar ‘online writers’ ba wato karancin sharhi.

Ya kika dauki rubutu a wajenki?
Nishadi, hanyar isar da sako cikin sauki.

Mene ne burinki na gaba game da rubutu?
Burina na gaba bai wuce in zama sananniyar marubuciya wacce duniya za ta yi alfahari da irin rubuce-rubucena ko bayan shudewa ta ba.

Ko akwai wanda ya taba bata miki rai ko faranta miki game da rubutu?

Uhm! Idan ma akwai wanda ya bata mini rai game da rubutuna to na manta, amma su na yabo ba na mantawa. Nakan yi mamaki sosai kuma na ji farinciki a duk lokacin da na ga manyan marubuta suna yaba rubutuna da kuma masu yi mini kallon allon kwaikwayonsu a fagen rubutu. Yadda rubutuna ke yawan samun yabo a ta bangarorin da ban yi tsammani ba. Da kuma yadda rubutu ya yi silar haduwata da manyan mutane (sarki, gwamna, matsimakiyar gwamna, da ma wasu cikin masu rike da mukaman gwamnati) har yanzu ji nake kamar a mafarki ne hakan ta faru.

Bayan rubutu kina wata sana’ar ne?
Eh, bayan rubutu ina taba sana’ar gashe-gashe, sayar da kayan sanyi a cikin gida, ina taba aikin jaridar online. A takaice dai ni komai da ruwanki ce in dai zan iya abin.

Ta ya ki ke iya hada ayyukanki da kuma rubutunki?
Sana’a, rubutu, karatu kowanne yana da nasa lokacin, in dai ka yi wa kanka tsari mai kyau. Don haka wannan bai taba zame mini damuwa ba.

Kamar wane irin lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?
Da dare, lokacin da sawu ya dauke nutsuwa ta sauko mini.

Me za ki ce da masu karanta labaranki?
Abin da zan ce musu shi ne sannun su da jimirin bibiyar rubutukana, Allah ya saka musu da alkhairi ya bar kauna. Ina matukar godiya da alfaharin kasancewar su tare da ni.

Gaida mutum biyar.
Sai dai mutum biyar sun yi karanci a gaisuwata don ko wadanda suka cancanci gaisuwar suna da tarin yawa, amma dai wadanda ba su ji sunan su ba su yi min afuwa duk kuna raina. Ina gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga; Yusuf Yahya Gumel, Bilkisu Muhammad Garkuwa, Jibril Adamu J. Rano, Maryama H, Fatima Sunusi Rabi’u.

Rukayya
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Masanan Singapore: Kasashen Kudu Maso Gabashin Asiya Sun Gamsu Da Huldarsu Da Kasar Sin

Masanan Singapore: Kasashen Kudu Maso Gabashin Asiya Sun Gamsu Da Huldarsu Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.