A yau Jumma’a, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, a duk irin kalubalen da za a iya samu daga waje, masana’antun kasar Sin za su ci gaba da zama ababen nema a duniya, kuma kasuwannin kasar za su kasance a ko yaushe masu jan hankali wajen zuba jarin waje.
An ba da rahoton cewa, a yanayin tangardar da tattalin arzikin kasa da kasa ke fuskanta, huldar kasuwanci da tattalin arzikin kasar Sin da sauran kasashen duniya na nan daram ko gezau. A cikin watanni biyar na farkon wannan shekara, kasar Sin ta bude hanyoyin sufurin jiragen sama na dakon kaya na kasa da kasa guda 101, kuma an kara yawan zirga-zirgar jiragen sama na mako-mako da fiye da 195.
Daga watan Janairu zuwa Afrilu, yawan kayayyakin da ake jigilarsu ta tashar jiragen ruwa na kasar Sin ya kai tan biliyan 5.755, wanda ya karu da kashi 3.7 bisa dari a mizanin shekara-shekara, kuma yawan kwantenoni masu fadin kafa 20 da aka yi jigilarsu ta tashar jiragen ruwan dakon kaya na kasar Sin ya zarce miliyan 110, wanda ya karu da kaso 7.9 bisa dari a mizanin kowace shekara.
Bugu da kari, jami’in ya ce, tattalin arzikin kasar Sin na ci gaba da nuna bajintar kuzarinsa, kuma yana kara samun karbuwa a harkokin kasuwanci cikin karfi. Inda hakan ke cikakken nuna cewa, a duk wani kalubale da za a iya samu daga waje, masana’antun kasar Sin za su ci gaba da zama ababen nema a duniya, kuma kasuwannin kasar ta Sin za su kasance masu jan hankali wajen zuba jarin waje. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp