Wani jami’in Hukumar Tsaron Sibil Difens da ke aiki a sansanin mahajjata a Yola, Abubakar Abdulkadir Mayos, ya mayar da kuɗin wata mata da suka faɗi.
Kuɗin sun haɗa da Dalar Amurka 505 da Riyal 30, waɗanda suka faɗi wanda mallakin wGa Hajiya Maimuna Salihu ce daga Jihar Taraba.
- Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600
- Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Jami’in ya tsinci kuɗin da safiyar ranar Asabar, 17 ga watan Mayu, ya kuma miƙa su cikin gaskiya.
An miƙa kuɗaɗen ne a gaban jami’an hukumar alhazai ta ƙasa (NAHCON), da wakilan hukumar jin daɗin alhazai ta Taraba, tare da wasu jami’an tsaro a sansanin.
Bayan gano kuɗin, jami’in ya sanar da hukumomi, sannan aka adana su har sai da aka gano mai su.
Mahajjata da jami’ai sun yaba da wannan gaskiya da rikon amana.
Wasu sun ce hakan ya ƙara musu ƙwarin gwiwa ga tsaron mahajjata da amincin tsarin aikin hajji.
“Alhamdulillah, Hajiya ta samu kuɗinta gaba ɗaya,” in ji wani jami’in sansanin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp