Jam’iyyar Labour (LP) ta fuskanci babban koma baya sakamakon ficewar wasu ‘yan majalisa guda biyar daga cikinta, suka kuma sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC a yau Alhamis.
Daga cikin waɗanda suka sauya sheƙar akwai Tochukwu Okere (Imo), da Donatus Mathew (Kaduna), a Bassey Akiba (Cross River), da Iyawe Esosa (Edo) da kuma Daulyop daga Filato
An tabbatar da sauya sheƙar tasu ne a lokacin zama na majalisa, inda Kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas, ya karanta wasiƙun sauya shekarsu a gaban taron.
- Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters
- Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido
Donatus Mathew, wanda ke wakiltar Kaura a Kaduna, ya bayyana dalilinsa na barin jam’iyyar LP a matsayin matakin kashin kai. Ya ce, ko da yake wannan shawara ba za ta yi wa dukkanin waɗanda suka zabe shi daɗi ba, amma wani yanayi ne domin alfanunsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp