• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Japan Ta Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Miliyan 108 A Matsayin Daukin Gaggawa Don Samar Da Abinci

byAbubakar Abba
9 months ago
Japan

Kasar Japan, ta bai wa Nijeriya bashin dala miliyan 108 a matsayin daukin gaggaka don samar da abinci a kasar.

Jakadar Kasar Japan, Yuka Furutani da ke ofishin Jakadancin kasar a nan Nijeriya ce ta sanar da hakan; a wani taron bita da aka shirya wa wasu malaman aikin gona ta hanyar fasahar zamani, wadda aka gudanar a Abuja.

  • Ya Kamata Tuba Daga Laifin Yaki Da Tsoffin Sojojin Japan Ke Yi Ya Zama Matsaya Guda Ta Daukacin ‘Yan Siyasar Japan
  • Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta

Hukumar Aikin Noma ta Afirka da ke bayar da shawara a fannin aikin noma (AFAAS), tare da hadin gwiwar Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da Cibiyar Aikin Noma ta Kimiyya (AGRA), da kamfanin tuntuba na Sahel da kuma shirin Aikin Noma na Afirka ne suka shirya taron a kwanakin baya.

Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta dauki nauyin shirin; wanda aka gudanar a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

A cewar Furutani, Gwamnatin Kasar Japan; na ci gaba da mayar da hankali wajen sama wa kasasehn Afirka da ke fama da karancin abinci bashi.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Ta sanar da cewa, a watan Afirilun 2024; Nijeriya da Japan, sun rabbata hannun yarjejeniya a wani taro na kasa da kasa da aka gudanar a Tokyo kan yadda Japan za ta samar da bashin dala miliyan 108 ga Nijeriya.

Kazalika, ta bayyana cewa; Japan ta kara fadada wannan bashin zuwa akalla dala miliyan 4.2, domin kara habaka samar da Irin noman Shinkafa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Daraktan Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da ke Nijeriya, Godwin Atser wanda ke jagorantar aikin ya bayyana cewa; Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta zuba makudan kudade; don gudanar da aikin, wanda kuma za a  gudanar da bincike a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

Godwin ya sanar da cewa, za a gudanar da binciken ne; domin gano adadi da kuma malaman aikin gona, musamman don lalubo mafitar da ake bukata ta bai wa kowane jinsi damar duba sauyin noma a Nijeriya, musamman a kan amfanin gona na Masara, Farin Wake, Rogo, Waken Suya da kuma a fannin dabbobi.

Muna da manhajar fasahar zamani iri-iri da aka samar da za iya amfani da su, don jawo manoma a jiki tare da ba su kariyar da ta dace”, in ji shi.

Godwin ya kuma yi nuni da cewa, idan aka kara habaka noma; hakan na nuna cewa, an tunkari turbar rage talauci a cikin al’umma, musamman duba da cewa; kashi 70 cikin 100 na a’lummar da ke zaune a karkara, sun dogara ne da fannin aikin noma.

Shi kuwa, Deola-Tayo Lordbanjou; Darakta a Hukumar Kula Bunkasa Ayyukan Malaman Aikin Gona ta Tarayya ya sanar da cewa, bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; akwai karancin ilimantarwa a fannin aikin noma a Nijeriya.

Deola-Tayo ya kara da cewa, malaman aikin gona sun fi yawa a shekarar 1980 a kasar, idan aka kwatanta da wadanda ake da su yanzu a fadin wannan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version