• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Japan Ta Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Miliyan 108 A Matsayin Daukin Gaggawa Don Samar Da Abinci

by Abubakar Abba
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Japan Ta Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Miliyan 108 A Matsayin Daukin Gaggawa Don Samar Da Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Japan, ta bai wa Nijeriya bashin dala miliyan 108 a matsayin daukin gaggaka don samar da abinci a kasar.

Jakadar Kasar Japan, Yuka Furutani da ke ofishin Jakadancin kasar a nan Nijeriya ce ta sanar da hakan; a wani taron bita da aka shirya wa wasu malaman aikin gona ta hanyar fasahar zamani, wadda aka gudanar a Abuja.

  • Ya Kamata Tuba Daga Laifin Yaki Da Tsoffin Sojojin Japan Ke Yi Ya Zama Matsaya Guda Ta Daukacin ‘Yan Siyasar Japan
  • Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta

Hukumar Aikin Noma ta Afirka da ke bayar da shawara a fannin aikin noma (AFAAS), tare da hadin gwiwar Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da Cibiyar Aikin Noma ta Kimiyya (AGRA), da kamfanin tuntuba na Sahel da kuma shirin Aikin Noma na Afirka ne suka shirya taron a kwanakin baya.

Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta dauki nauyin shirin; wanda aka gudanar a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

A cewar Furutani, Gwamnatin Kasar Japan; na ci gaba da mayar da hankali wajen sama wa kasasehn Afirka da ke fama da karancin abinci bashi.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Ta sanar da cewa, a watan Afirilun 2024; Nijeriya da Japan, sun rabbata hannun yarjejeniya a wani taro na kasa da kasa da aka gudanar a Tokyo kan yadda Japan za ta samar da bashin dala miliyan 108 ga Nijeriya.

Kazalika, ta bayyana cewa; Japan ta kara fadada wannan bashin zuwa akalla dala miliyan 4.2, domin kara habaka samar da Irin noman Shinkafa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Daraktan Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da ke Nijeriya, Godwin Atser wanda ke jagorantar aikin ya bayyana cewa; Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta zuba makudan kudade; don gudanar da aikin, wanda kuma za a  gudanar da bincike a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

Godwin ya sanar da cewa, za a gudanar da binciken ne; domin gano adadi da kuma malaman aikin gona, musamman don lalubo mafitar da ake bukata ta bai wa kowane jinsi damar duba sauyin noma a Nijeriya, musamman a kan amfanin gona na Masara, Farin Wake, Rogo, Waken Suya da kuma a fannin dabbobi.

Muna da manhajar fasahar zamani iri-iri da aka samar da za iya amfani da su, don jawo manoma a jiki tare da ba su kariyar da ta dace”, in ji shi.

Godwin ya kuma yi nuni da cewa, idan aka kara habaka noma; hakan na nuna cewa, an tunkari turbar rage talauci a cikin al’umma, musamman duba da cewa; kashi 70 cikin 100 na a’lummar da ke zaune a karkara, sun dogara ne da fannin aikin noma.

Shi kuwa, Deola-Tayo Lordbanjou; Darakta a Hukumar Kula Bunkasa Ayyukan Malaman Aikin Gona ta Tarayya ya sanar da cewa, bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; akwai karancin ilimantarwa a fannin aikin noma a Nijeriya.

Deola-Tayo ya kara da cewa, malaman aikin gona sun fi yawa a shekarar 1980 a kasar, idan aka kwatanta da wadanda ake da su yanzu a fadin wannan kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Japan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakiya Kan Harkokin Siyasa Ga Gwamnan Kaduna, Rachael Averik, Ta Tsallake Rijiya Da Baya

Next Post

Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

7 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.