ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Japan Ta Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Miliyan 108 A Matsayin Daukin Gaggawa Don Samar Da Abinci

by Abubakar Abba
2 years ago
Japan

Kasar Japan, ta bai wa Nijeriya bashin dala miliyan 108 a matsayin daukin gaggaka don samar da abinci a kasar.

Jakadar Kasar Japan, Yuka Furutani da ke ofishin Jakadancin kasar a nan Nijeriya ce ta sanar da hakan; a wani taron bita da aka shirya wa wasu malaman aikin gona ta hanyar fasahar zamani, wadda aka gudanar a Abuja.

  • Ya Kamata Tuba Daga Laifin Yaki Da Tsoffin Sojojin Japan Ke Yi Ya Zama Matsaya Guda Ta Daukacin ‘Yan Siyasar Japan
  • Da Alamu Japan Ta Shirya Gyara Kuskurenta

Hukumar Aikin Noma ta Afirka da ke bayar da shawara a fannin aikin noma (AFAAS), tare da hadin gwiwar Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da Cibiyar Aikin Noma ta Kimiyya (AGRA), da kamfanin tuntuba na Sahel da kuma shirin Aikin Noma na Afirka ne suka shirya taron a kwanakin baya.

ADVERTISEMENT

Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta dauki nauyin shirin; wanda aka gudanar a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

A cewar Furutani, Gwamnatin Kasar Japan; na ci gaba da mayar da hankali wajen sama wa kasasehn Afirka da ke fama da karancin abinci bashi.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ta sanar da cewa, a watan Afirilun 2024; Nijeriya da Japan, sun rabbata hannun yarjejeniya a wani taro na kasa da kasa da aka gudanar a Tokyo kan yadda Japan za ta samar da bashin dala miliyan 108 ga Nijeriya.

Kazalika, ta bayyana cewa; Japan ta kara fadada wannan bashin zuwa akalla dala miliyan 4.2, domin kara habaka samar da Irin noman Shinkafa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Daraktan Kungiyar Aikin Noma ta Afirka Sasakawa da ke Nijeriya, Godwin Atser wanda ke jagorantar aikin ya bayyana cewa; Gidauniyar Bill da Melinda Gates ce, ta zuba makudan kudade; don gudanar da aikin, wanda kuma za a  gudanar da bincike a Jihohin Oyo, Gombe da kuma Kaduna.

Godwin ya sanar da cewa, za a gudanar da binciken ne; domin gano adadi da kuma malaman aikin gona, musamman don lalubo mafitar da ake bukata ta bai wa kowane jinsi damar duba sauyin noma a Nijeriya, musamman a kan amfanin gona na Masara, Farin Wake, Rogo, Waken Suya da kuma a fannin dabbobi.

Muna da manhajar fasahar zamani iri-iri da aka samar da za iya amfani da su, don jawo manoma a jiki tare da ba su kariyar da ta dace”, in ji shi.

Godwin ya kuma yi nuni da cewa, idan aka kara habaka noma; hakan na nuna cewa, an tunkari turbar rage talauci a cikin al’umma, musamman duba da cewa; kashi 70 cikin 100 na a’lummar da ke zaune a karkara, sun dogara ne da fannin aikin noma.

Shi kuwa, Deola-Tayo Lordbanjou; Darakta a Hukumar Kula Bunkasa Ayyukan Malaman Aikin Gona ta Tarayya ya sanar da cewa, bisa wani bincike da aka gudanar, an gano cewa; akwai karancin ilimantarwa a fannin aikin noma a Nijeriya.

Deola-Tayo ya kara da cewa, malaman aikin gona sun fi yawa a shekarar 1980 a kasar, idan aka kwatanta da wadanda ake da su yanzu a fadin wannan kasa.

Japan
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

Babban jami’in JKS Ya Yi Kira Da A Nazarci Kuma A Aiwatar Da Tunanin Xi Jinping Kan Al’adu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.