• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Da Sinawa ‘Yan Kasuwa Masu Zaman Kansu Ke Zubawa A Angola Na Bunkasa Rayuwar ‘Yan Kasar

by CGTN Hausa
2 years ago
Angola

Karamin ministan tsare tsaren tattalin arziki na kasar Angola Jose de Lima Massano, ya jinjinawa tasirin jarin Sinawa ‘yan kasuwa a Angola, wanda a cewar ministan ya taimaka matuka wajen kyautata rayuwar al’ummar kasar.

Mista Massano, ya bayyana hakan ne yayin taron kungiyar raya cinikayya ta Angola da Sin ko CAC, da kamfanoni mambobin kungiyar, wanda ya gudana ranar Asabar a birnin Luanda, fadar mulkin Angola. Ya ce kamfanonin ‘yan kasuwa Sinawa masu zaman kan su, sun zuba jari a Angola wanda hakan ya haifar da damammakin samun kudin shiga ga ‘yan kasar.

  • Kasar Sin Ta Aike Da Kayayyakin Agajin Gaggawa Zuwa Kasar Libya Da Ambaliyar Ruwa Ta Afkawa
  • Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Kaza lika, mista Massano ya ce dalilin gudanar da taron shi ne bunkasa tattaunawa tsakanin kamfanonin Sin da na Angola, da sashen raya tattalin arziki na gwamnatin kasar.

A nasa tsokaci, shugaban CAC Luis Cupenala, wanda ke wakiltar kamfanonin Sinawa masu zaman kan su a taron, ya gabatar da bayanai da shawarwari, ciki har da batun yarjejeniyoyin kare jarin da aka zuba, da kyautata tsarin fitar da hajoji, da inganta yanayin gudanar da kasuwanci.

Game da hakan, mista Massano ya ce gwamnatin Angola, za ta ci gaba da warware wadannan batutuwa, da taimakawa kamfanoni wajen kawar da kalubalen da ake fuskanta, da kara inganta yanayin gudanar da kasuwanci ga kamfanonin ketare masu zaman kan su, ta yadda hakan zai bunkasa dunkulewar sassan ci gaban Angola. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Next Post
Filato

Shugaban Karamar Hukuma Ya Yi Tir Da Kisan Jagoran Fulani Dan Shekara 70 A Jihar Filato

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.