• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

by CMG Hausa
2 years ago
Habasha

Kasar Habasha dake yankin kahon Afirka, na cikin kasashen nahiyar Afirka dake kan gaba wajen cin gajiya daga jarin waje na kasar Sin, inda tuni kasar ta fara more manyan ababen more rayuwa da Sin ta gina karkashin shirye-shiryen raya kasa daban daban, ciki har da shawarar “ziri daya da hanya daya”, wadanda suka haifar da gagarumin sauyi a fannin raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar.

Karkashin irin wadannan manufofi, a halin yanzu kasar Habasha na more ribar kyautatuwar sufurin jiragen kasa na zamani da kasar Sin ta gina, wadanda ke zirga-zirga cikin kasar da ma makwafciyar ta kasar Djibouti. Kuma hakan na zuwa ne a gabar da Habashan ke fatan samun karin jari daga sassa daban daban na kasar Sin.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Ko shakka babu irin yadda mahukuntan kasar Habasha ke bayyana kyakkyawan fata ga shigar karin jarin Sin cikin kasar, ya shaida gamsuwa da kasar ta yi da nasarorin da ta cimma bisa hadin gwiwarta da Sin.

Ga duk wanda ke bibbiyar ci gaban yankin kahon Afirka, yana iya shaida manyan nasarori da Habasha ta cimma a bangaren sufuri na zamani, da kafuwar yankin masana’antu na zamani, wanda ya baiwa kasar damar sarrafa hajoji da dama da ake amfani da su a cikin kasar da ma sauran kasashen Afirka.

A hakin yanzu kuma, Habasha na fatan kara fadada hadin gwiwa da sassan kasar Sin, wajen bunkasa harkokin sarrafa hajoji, da samar da makamashi mai tsafta, da inganta noma bisa dabarun zamani. A hannu guda kuma, kasar wadda ta zama a sahun gaba a Afirka wajen yawan cinikayya, da zuba jari tsakaninta da Sin cikin shekaru masu yawa da suka gabata, tana kuma amfani da wannan zarafi wajen bunkasa hada hadar fitar da hajojinta zuwa kasar Sin, da ma sauran sassan duniya masu yawa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Tabbas sassan kasar Sin dake zuba jari a Habasha, sun taka rawar gani a fannin samar da guraben ayyukan yi, da bunkasa fasahohin wanzar da ci gaba, don haka ma masharhanta da dama ke ganin masu zuba jari na Sin a kasar Habasha, baya ga kasancewar su masu samar da kudade, sun kuma zamo muhimmin bangare na hadin gwiwar kasar, wajen warware kalubalen tattalin arziki da zamantakewa, duba da yadda suke taimakawa Habasha da jari kai tsaye, ba tare da la’akari da yawan riba ko gindaya wasu sharudda na siyasa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu 'Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.