• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Habasha dake yankin kahon Afirka, na cikin kasashen nahiyar Afirka dake kan gaba wajen cin gajiya daga jarin waje na kasar Sin, inda tuni kasar ta fara more manyan ababen more rayuwa da Sin ta gina karkashin shirye-shiryen raya kasa daban daban, ciki har da shawarar “ziri daya da hanya daya”, wadanda suka haifar da gagarumin sauyi a fannin raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar.

Karkashin irin wadannan manufofi, a halin yanzu kasar Habasha na more ribar kyautatuwar sufurin jiragen kasa na zamani da kasar Sin ta gina, wadanda ke zirga-zirga cikin kasar da ma makwafciyar ta kasar Djibouti. Kuma hakan na zuwa ne a gabar da Habashan ke fatan samun karin jari daga sassa daban daban na kasar Sin.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Ko shakka babu irin yadda mahukuntan kasar Habasha ke bayyana kyakkyawan fata ga shigar karin jarin Sin cikin kasar, ya shaida gamsuwa da kasar ta yi da nasarorin da ta cimma bisa hadin gwiwarta da Sin.

Ga duk wanda ke bibbiyar ci gaban yankin kahon Afirka, yana iya shaida manyan nasarori da Habasha ta cimma a bangaren sufuri na zamani, da kafuwar yankin masana’antu na zamani, wanda ya baiwa kasar damar sarrafa hajoji da dama da ake amfani da su a cikin kasar da ma sauran kasashen Afirka.

A hakin yanzu kuma, Habasha na fatan kara fadada hadin gwiwa da sassan kasar Sin, wajen bunkasa harkokin sarrafa hajoji, da samar da makamashi mai tsafta, da inganta noma bisa dabarun zamani. A hannu guda kuma, kasar wadda ta zama a sahun gaba a Afirka wajen yawan cinikayya, da zuba jari tsakaninta da Sin cikin shekaru masu yawa da suka gabata, tana kuma amfani da wannan zarafi wajen bunkasa hada hadar fitar da hajojinta zuwa kasar Sin, da ma sauran sassan duniya masu yawa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Tabbas sassan kasar Sin dake zuba jari a Habasha, sun taka rawar gani a fannin samar da guraben ayyukan yi, da bunkasa fasahohin wanzar da ci gaba, don haka ma masharhanta da dama ke ganin masu zuba jari na Sin a kasar Habasha, baya ga kasancewar su masu samar da kudade, sun kuma zamo muhimmin bangare na hadin gwiwar kasar, wajen warware kalubalen tattalin arziki da zamantakewa, duba da yadda suke taimakawa Habasha da jari kai tsaye, ba tare da la’akari da yawan riba ko gindaya wasu sharudda na siyasa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Next Post

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

19 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu 'Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.