• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Habasha dake yankin kahon Afirka, na cikin kasashen nahiyar Afirka dake kan gaba wajen cin gajiya daga jarin waje na kasar Sin, inda tuni kasar ta fara more manyan ababen more rayuwa da Sin ta gina karkashin shirye-shiryen raya kasa daban daban, ciki har da shawarar “ziri daya da hanya daya”, wadanda suka haifar da gagarumin sauyi a fannin raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar.

Karkashin irin wadannan manufofi, a halin yanzu kasar Habasha na more ribar kyautatuwar sufurin jiragen kasa na zamani da kasar Sin ta gina, wadanda ke zirga-zirga cikin kasar da ma makwafciyar ta kasar Djibouti. Kuma hakan na zuwa ne a gabar da Habashan ke fatan samun karin jari daga sassa daban daban na kasar Sin.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Ko shakka babu irin yadda mahukuntan kasar Habasha ke bayyana kyakkyawan fata ga shigar karin jarin Sin cikin kasar, ya shaida gamsuwa da kasar ta yi da nasarorin da ta cimma bisa hadin gwiwarta da Sin.

Ga duk wanda ke bibbiyar ci gaban yankin kahon Afirka, yana iya shaida manyan nasarori da Habasha ta cimma a bangaren sufuri na zamani, da kafuwar yankin masana’antu na zamani, wanda ya baiwa kasar damar sarrafa hajoji da dama da ake amfani da su a cikin kasar da ma sauran kasashen Afirka.

A hakin yanzu kuma, Habasha na fatan kara fadada hadin gwiwa da sassan kasar Sin, wajen bunkasa harkokin sarrafa hajoji, da samar da makamashi mai tsafta, da inganta noma bisa dabarun zamani. A hannu guda kuma, kasar wadda ta zama a sahun gaba a Afirka wajen yawan cinikayya, da zuba jari tsakaninta da Sin cikin shekaru masu yawa da suka gabata, tana kuma amfani da wannan zarafi wajen bunkasa hada hadar fitar da hajojinta zuwa kasar Sin, da ma sauran sassan duniya masu yawa.

Labarai Masu Nasaba

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Tabbas sassan kasar Sin dake zuba jari a Habasha, sun taka rawar gani a fannin samar da guraben ayyukan yi, da bunkasa fasahohin wanzar da ci gaba, don haka ma masharhanta da dama ke ganin masu zuba jari na Sin a kasar Habasha, baya ga kasancewar su masu samar da kudade, sun kuma zamo muhimmin bangare na hadin gwiwar kasar, wajen warware kalubalen tattalin arziki da zamantakewa, duba da yadda suke taimakawa Habasha da jari kai tsaye, ba tare da la’akari da yawan riba ko gindaya wasu sharudda na siyasa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Next Post

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

Related

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

57 minutes ago
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

2 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

3 hours ago
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

4 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

5 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

6 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu 'Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.