ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kubutar Da Wasu ‘Yan Matan Chibok 2 Bayan Shekara 9 A Hannun Boko Haram

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Dakarun Operation Hadin Kai sun ceto wasu ‘yan mata biyu da aka sace daga karamar hukumar Chibok ta Jihar Borno a watan Afrilun 2014.

Wannan ceton ya zo ne shekaru tara da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kai hari makarantarsu a lokacin da suke rubuta jarabawar kammala sakandare.

  • A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar
  • Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

An kula da wadanda abin ya shafa – Esther Marcus da Hauwa Malta, dukkansu masu shekaru 26 – yayin da sojoji suka ceto su a Lagara, wani yanki na ‘yan Boko Haram da ke dajin Sambisa, a ranar 21 ga Afrilu, 2023.

ADVERTISEMENT

Ceton na baya-bayan nan, adadin ‘yan matan da aka yi garkuwa da su yanzu ya kai 125, ciki har da 107 da ‘yan ta’addan suka sake su a shekarar 2018, uku da sojoji suka ceto a shekarar 2019, biyu a shekarar 2021, da kuma 11 a shekarar 2022.

A cewar kwamandan Operation Hadin Kai, Manjo Janar Ibrahim Sallau Ali, “har yanzu ba a gano 94 ba.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“An ceto Esther tare da ‘yarta ‘yar shekara daya. Yayin da ake garkuwa da ita, ta auri wani Garba, wanda ake kira Garus, dan ta’adda, wanda daga baya sojoji suka kashe; sannan wani dan ta’adda mai suna Abba ya aure ta; tana tare da shi har zuwa lokacin da aka ceto ta.”

Kwamandan ya bayyana cewa an ceto Hauwa Malta da cikin wata takwas da kwana 10; ta kara da cewa ta haifi wani yaro a cibiyar lafiya ta Seven Div kwanaki 10 bayan ceto su.

Sojojin sun kuma kashe sama da mutane 70 da ake zargin ‘yan ta’adda ne a farmakin da suka kai a yankin Arewa maso Gabas.

An kuma kama sama da ‘yan ta’adda 140 a tsawon lokacin, tare da kwato makamai da dama da suka hada da nakiya, kamar yadda daraktan ayyukan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Musa Danmadami ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Masanin Kasar Afrika Ta Kudu Ya Bayyana Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

Masanin Kasar Afrika Ta Kudu Ya Bayyana Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.