• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

by Rabilu Sanusi Bena
12 months ago
in Nishadi
0
Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake ci gaba da kirga asarori da rayukan da aka rasa sakamakon wata mummunar ambaliya da aka yi a birnin Maiduguri fadar gwamnatin Jihar Borno, mutane da dama na nuna alhini da tausayawa ga wadannan mutane da abin ya shafa.

Daga cikin masu wannan jajantawa akwai jarumai a masana’antar Kannywood wadanda suka nuna alhini a bayyane suka kuma jajantawa gwamnati da kuma al’ummar jahar Borno.

  • Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7
  • Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

Ali Nuhu

Jarumai

Daga cikin jaruman da suka jajanta wa al’ummar Jihar Borno akwai shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya kuma jarumi a masana’antar Kannywood Ali Nuhu Muhammad inda ya ce “Ina mika sakon jaje da kuma alhini ga mutanen da ambaliyar ruwa ya shafa a Jahar Borno da sauran yankunan kasar nan, Allah ya kawo mana saukin wannan al’amarin”.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Abba El Mustapha

Jarumai

 

Haka zalika akwai shugaban hukumar ta ce fina finai da dab’i na jahar Kano Abba El Mustapha shima ya jajantawa wadannan bayin Allah da ambaliyar ruwa ta shafa,a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Facebook El Mustapha ya ce “Wallahi, da garin MAIDUGURI na Kwana na kuma tashi a raina. Ya Allah ka kawo musu mafuta ta ALHERI kasa IBTILA’IN da ya faru dasu ya zama kaffara”.

Sani Musa Danja

Akwai kuma jarumi kuma tsohon dan takarar shugaban karamar hukumar Nassarawa da ke Jihar Kano Sani Musa Danja inda a wani faifan bidiyo da aka dora a shafukan zumunta ya ke cewa a madadin masana’antar Kannywood ya na jajantawa al’ummar birnin Maiduguri da ma jahar Borno baki daya, ya na fatan duk wadanda suka rasa dukiyoyins Allah ya mayar masu da mafificin alheri.

Aminu Ladan Abubakar (ALA)

Jarumai

Daya daga cikin dattawan mawaka a masana’antar Kannywood Aminu Ladan Abubakar wanda akafi sani da Ala shima ba a barshi a baya ba wajen jajantawa wadannan bayin Allah da iftila’in ruwa ya shafa,inda ya roki Allah ya gafarta wa wazanda suka rasa rayukansu ya kuma mayar da alheri ga mutanen da suka yi asarar dukiyoyinsu.

Dauda Kahutu Rarara

Jarumai

Mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara na daga cikin wadanda suka bayar da gudunmawar addu’a da kuma aljihunsu,Rarara ya jajantawa al’ummar jahar Borno da kuma mutanen Maiduguri da abin ya shafa,haka zalika ya bayar da gudunmawar abinci da sauran kayan amfani ga wani rukuni na masu gudun hijira a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JajeJarumaiKannywoodMaiduguri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

Next Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

3 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.