• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

by Rabilu Sanusi Bena
10 months ago
in Nishadi
0
Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake ci gaba da kirga asarori da rayukan da aka rasa sakamakon wata mummunar ambaliya da aka yi a birnin Maiduguri fadar gwamnatin Jihar Borno, mutane da dama na nuna alhini da tausayawa ga wadannan mutane da abin ya shafa.

Daga cikin masu wannan jajantawa akwai jarumai a masana’antar Kannywood wadanda suka nuna alhini a bayyane suka kuma jajantawa gwamnati da kuma al’ummar jahar Borno.

  • Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7
  • Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

Ali Nuhu

Jarumai

Daga cikin jaruman da suka jajanta wa al’ummar Jihar Borno akwai shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya kuma jarumi a masana’antar Kannywood Ali Nuhu Muhammad inda ya ce “Ina mika sakon jaje da kuma alhini ga mutanen da ambaliyar ruwa ya shafa a Jahar Borno da sauran yankunan kasar nan, Allah ya kawo mana saukin wannan al’amarin”.

Labarai Masu Nasaba

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Abba El Mustapha

Jarumai

 

Haka zalika akwai shugaban hukumar ta ce fina finai da dab’i na jahar Kano Abba El Mustapha shima ya jajantawa wadannan bayin Allah da ambaliyar ruwa ta shafa,a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Facebook El Mustapha ya ce “Wallahi, da garin MAIDUGURI na Kwana na kuma tashi a raina. Ya Allah ka kawo musu mafuta ta ALHERI kasa IBTILA’IN da ya faru dasu ya zama kaffara”.

Sani Musa Danja

Akwai kuma jarumi kuma tsohon dan takarar shugaban karamar hukumar Nassarawa da ke Jihar Kano Sani Musa Danja inda a wani faifan bidiyo da aka dora a shafukan zumunta ya ke cewa a madadin masana’antar Kannywood ya na jajantawa al’ummar birnin Maiduguri da ma jahar Borno baki daya, ya na fatan duk wadanda suka rasa dukiyoyins Allah ya mayar masu da mafificin alheri.

Aminu Ladan Abubakar (ALA)

Jarumai

Daya daga cikin dattawan mawaka a masana’antar Kannywood Aminu Ladan Abubakar wanda akafi sani da Ala shima ba a barshi a baya ba wajen jajantawa wadannan bayin Allah da iftila’in ruwa ya shafa,inda ya roki Allah ya gafarta wa wazanda suka rasa rayukansu ya kuma mayar da alheri ga mutanen da suka yi asarar dukiyoyinsu.

Dauda Kahutu Rarara

Jarumai

Mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara na daga cikin wadanda suka bayar da gudunmawar addu’a da kuma aljihunsu,Rarara ya jajantawa al’ummar jahar Borno da kuma mutanen Maiduguri da abin ya shafa,haka zalika ya bayar da gudunmawar abinci da sauran kayan amfani ga wani rukuni na masu gudun hijira a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JajeJarumaiKannywoodMaiduguri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

Next Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Related

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

1 week ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

3 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

4 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

4 weeks ago
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 month ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Next Post
Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.