• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
in Nishadi
0
Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ake ci gaba da kirga asarori da rayukan da aka rasa sakamakon wata mummunar ambaliya da aka yi a birnin Maiduguri fadar gwamnatin Jihar Borno, mutane da dama na nuna alhini da tausayawa ga wadannan mutane da abin ya shafa.

Daga cikin masu wannan jajantawa akwai jarumai a masana’antar Kannywood wadanda suka nuna alhini a bayyane suka kuma jajantawa gwamnati da kuma al’ummar jahar Borno.

  • Sama Da Kasashe Da Hukumomin Kasa Da Kasa 70 Sun Ba Da Tabbacin Halartar Bikin CIIE Karo Na 7
  • Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

Ali Nuhu

Jarumai

Daga cikin jaruman da suka jajanta wa al’ummar Jihar Borno akwai shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya kuma jarumi a masana’antar Kannywood Ali Nuhu Muhammad inda ya ce “Ina mika sakon jaje da kuma alhini ga mutanen da ambaliyar ruwa ya shafa a Jahar Borno da sauran yankunan kasar nan, Allah ya kawo mana saukin wannan al’amarin”.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Abba El Mustapha

Jarumai

 

Haka zalika akwai shugaban hukumar ta ce fina finai da dab’i na jahar Kano Abba El Mustapha shima ya jajantawa wadannan bayin Allah da ambaliyar ruwa ta shafa,a wani rubutu da ya yi a shafinsa na Facebook El Mustapha ya ce “Wallahi, da garin MAIDUGURI na Kwana na kuma tashi a raina. Ya Allah ka kawo musu mafuta ta ALHERI kasa IBTILA’IN da ya faru dasu ya zama kaffara”.

Sani Musa Danja

Akwai kuma jarumi kuma tsohon dan takarar shugaban karamar hukumar Nassarawa da ke Jihar Kano Sani Musa Danja inda a wani faifan bidiyo da aka dora a shafukan zumunta ya ke cewa a madadin masana’antar Kannywood ya na jajantawa al’ummar birnin Maiduguri da ma jahar Borno baki daya, ya na fatan duk wadanda suka rasa dukiyoyins Allah ya mayar masu da mafificin alheri.

Aminu Ladan Abubakar (ALA)

Jarumai

Daya daga cikin dattawan mawaka a masana’antar Kannywood Aminu Ladan Abubakar wanda akafi sani da Ala shima ba a barshi a baya ba wajen jajantawa wadannan bayin Allah da iftila’in ruwa ya shafa,inda ya roki Allah ya gafarta wa wazanda suka rasa rayukansu ya kuma mayar da alheri ga mutanen da suka yi asarar dukiyoyinsu.

Dauda Kahutu Rarara

Jarumai

Mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara na daga cikin wadanda suka bayar da gudunmawar addu’a da kuma aljihunsu,Rarara ya jajantawa al’ummar jahar Borno da kuma mutanen Maiduguri da abin ya shafa,haka zalika ya bayar da gudunmawar abinci da sauran kayan amfani ga wani rukuni na masu gudun hijira a Maiduguri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JajeJarumaiKannywoodMaiduguri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

Next Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

5 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.