ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

by Abubakar Abba
2 years ago
Fyade

Wasu masu kare hakkin ‘yan Adam a Jihar Kaduna sun shigar da kara a gaban kotun Majistari da ke da zama a titin Daura Road, mai lamba 37.

Sun shigar da karar ce, don kotun ta sake bude shari’ar yaron nan Almajiri dan shekara 13 da wani mai suna Isah Abdullah daya daga cikin hadimin ‘yar majalsair dokin jihar Kaduna Munirat Suleiman mai wakilitar mazabar Saminaka ya yi wa fyade.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

A cewasu, ba su amince da wancan hukukuncin da alkalin kotun Majistari mai lamba 2 Mai Shari’a Aliyu Dogara ya yanke na wanke Isah Abdullah da kuma sakinsa ba.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, binciken da sashin manyan laifuka na rundunar ‘yansandan a Jihar Kaduna ya yi, a kan zargin ya gabatar da Isa gaban kotun mai lamba 2, wanda kotun ta bayar da umarni a ajiye Isah a gidan gyaran hali na jihar, kafin ma’aikatar Shari’ar jihar ta bayar da shawara a kan zargin.

Amma bayan jiran shawara daga ma’aikatar Shara’a ta jihar, ta wanke Isa a sakamakon rahoton gwaji da aka samu daga Asibiti a Saminaka da kuma Asibitin koyarwa na Barau Dikko.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Sai dai, masu kare rajin hakkin ‘yan’adam a jihar, sun bayyana cewa, ba su amince da wancan hukuncin kotun da kuma takardun gwajin lafiyar yaron da Asibitin Barau Dikko da Garin Saminaka suka yi a kan Almajirin ba, inda suka sake garzayawa kotun ta Majistari da ke mai lamba 37, don ta bude Shari’ar.

A hirarsa da ‘yan jarida a Kaduna daya daga cikin masu kare rajin Marwan Yabo ya ce, wancan hukuncin da kotun Daura Road mai lamba 2 ta yanke bamu yarda da shi ba.

A cewarsa, masu kare wanda ake zargin a gaban kotun, sun yi amfani da wasu takardun da aka yiwa yaron gwaji ne, a wani Asibiti da ke a Saminaka da kuma gwajin da aka yi, a Asibitin Barau Dikko, kuma takardun gwajin da aka yi, a wadannan Asibitocin biyu, na hannun mu.

Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wasu takardu biyu wadanda suke nuna cewa, wai daga Asibitin Saminaka da kuma na Barau Dikko ne, aka bayar.

Ya kara da cewa, “To amma bamu san yadda aka yi suka samo wadannan takardun biyu ba, domin Asibitin Barau Dikko, a baya da kansu ne suka yi wa yaron gwaji suka kuma tura shi zuwa Asibitin kashi na Dala, da ke a Kano don a yi wa yaron aiki”.

Ya ce, bayan kotun mai lamba 2 ta bayar da umarnin cewa, a ajiye Isah a gidan gyran hali na jihar har sai yaron ya samu lafiya kafin a fara shari’ar, sai kawai muka ji cewa, wai kotun mai lamba 2 ta wanke Isah daga zargin, alhali ba a ma fara shariar gadan-gadan ba, kuma ba ji ta bakin yaron a kan me ya faru ba.

Shi ma daya mai kare hakiin ‘yan’adam kuma lauyan yaron Barista Sani Shehu a zantawarsa da ‘yanjarida ya ce, za su tabbatar an binciki wancan hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke, inda ya kara da cewa,”Muna zargin akwai shubuha a cikin hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke”.

Ya ce, idan har ita ma’aikatar shari’a ta kamar yadda takardun suka nuna cewa, ta dogara ne da wasu takardu na likita wadanda mai yiwuwa, wadancan takardun na likitan an kawo su ne ta bayan fage, ma’aikatar kuma ta yi abin da ta yi, doka ta bamu damar muma mu sake bude wata sabuwar shari’a.

Ya ce, ita kuma kotun da ta wanke wanda ake zargin, “Muna da ikon mu nemi kotu ta sama, ta warware wancan hukuncin na kotun ta 2, don a sake wani bincike don mu gabatar da dalilanmu”.

Fyade
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Matafiyi Obobo Ya Rasu

Matafiyi Obobo Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.