ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

by Abubakar Abba
2 years ago
Fyade

Wasu masu kare hakkin ‘yan Adam a Jihar Kaduna sun shigar da kara a gaban kotun Majistari da ke da zama a titin Daura Road, mai lamba 37.

Sun shigar da karar ce, don kotun ta sake bude shari’ar yaron nan Almajiri dan shekara 13 da wani mai suna Isah Abdullah daya daga cikin hadimin ‘yar majalsair dokin jihar Kaduna Munirat Suleiman mai wakilitar mazabar Saminaka ya yi wa fyade.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

A cewasu, ba su amince da wancan hukukuncin da alkalin kotun Majistari mai lamba 2 Mai Shari’a Aliyu Dogara ya yanke na wanke Isah Abdullah da kuma sakinsa ba.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, binciken da sashin manyan laifuka na rundunar ‘yansandan a Jihar Kaduna ya yi, a kan zargin ya gabatar da Isa gaban kotun mai lamba 2, wanda kotun ta bayar da umarni a ajiye Isah a gidan gyaran hali na jihar, kafin ma’aikatar Shari’ar jihar ta bayar da shawara a kan zargin.

Amma bayan jiran shawara daga ma’aikatar Shara’a ta jihar, ta wanke Isa a sakamakon rahoton gwaji da aka samu daga Asibiti a Saminaka da kuma Asibitin koyarwa na Barau Dikko.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Sai dai, masu kare rajin hakkin ‘yan’adam a jihar, sun bayyana cewa, ba su amince da wancan hukuncin kotun da kuma takardun gwajin lafiyar yaron da Asibitin Barau Dikko da Garin Saminaka suka yi a kan Almajirin ba, inda suka sake garzayawa kotun ta Majistari da ke mai lamba 37, don ta bude Shari’ar.

A hirarsa da ‘yan jarida a Kaduna daya daga cikin masu kare rajin Marwan Yabo ya ce, wancan hukuncin da kotun Daura Road mai lamba 2 ta yanke bamu yarda da shi ba.

A cewarsa, masu kare wanda ake zargin a gaban kotun, sun yi amfani da wasu takardun da aka yiwa yaron gwaji ne, a wani Asibiti da ke a Saminaka da kuma gwajin da aka yi, a Asibitin Barau Dikko, kuma takardun gwajin da aka yi, a wadannan Asibitocin biyu, na hannun mu.

Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wasu takardu biyu wadanda suke nuna cewa, wai daga Asibitin Saminaka da kuma na Barau Dikko ne, aka bayar.

Ya kara da cewa, “To amma bamu san yadda aka yi suka samo wadannan takardun biyu ba, domin Asibitin Barau Dikko, a baya da kansu ne suka yi wa yaron gwaji suka kuma tura shi zuwa Asibitin kashi na Dala, da ke a Kano don a yi wa yaron aiki”.

Ya ce, bayan kotun mai lamba 2 ta bayar da umarnin cewa, a ajiye Isah a gidan gyran hali na jihar har sai yaron ya samu lafiya kafin a fara shari’ar, sai kawai muka ji cewa, wai kotun mai lamba 2 ta wanke Isah daga zargin, alhali ba a ma fara shariar gadan-gadan ba, kuma ba ji ta bakin yaron a kan me ya faru ba.

Shi ma daya mai kare hakiin ‘yan’adam kuma lauyan yaron Barista Sani Shehu a zantawarsa da ‘yanjarida ya ce, za su tabbatar an binciki wancan hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke, inda ya kara da cewa,”Muna zargin akwai shubuha a cikin hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke”.

Ya ce, idan har ita ma’aikatar shari’a ta kamar yadda takardun suka nuna cewa, ta dogara ne da wasu takardu na likita wadanda mai yiwuwa, wadancan takardun na likitan an kawo su ne ta bayan fage, ma’aikatar kuma ta yi abin da ta yi, doka ta bamu damar muma mu sake bude wata sabuwar shari’a.

Ya ce, ita kuma kotun da ta wanke wanda ake zargin, “Muna da ikon mu nemi kotu ta sama, ta warware wancan hukuncin na kotun ta 2, don a sake wani bincike don mu gabatar da dalilanmu”.

Fyade
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Matafiyi Obobo Ya Rasu

Matafiyi Obobo Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.