• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar yada labarai ta Forbes ta bayyana sunayen wadanda suka zama attajirai mafiya arziki a Nijeriya a shekarar 2024. Su ne: Aliko Dangote, Mike Adenuga, Abdulsamad Rabiu, da Femi Otedola.

Kafar ta bayyana cewa Arzikin Dangote ya haura zuwa Dala biliyan 13.4, na Adenuga ya kai Dala biliyan 6.7, yayin da Abdulsalam Rabiu yake da Dala biliyan 5.2 shi kuma Otedola yake da dala biliyan 1.4.

  • Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya

Aliko Dangote shi ne mutumin da ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka kuma bakar fata mafi arziki a duniya, inda aka kiyasta kudinsa ya kai kusan dala biliyan 13.4 a shekarar 2024. Katafaren kasuwancinsa na rukunnan kamfanin Dangote Group, na daya daga cikin manyan kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya kuma kamfani mafi daraja a Afirka ta Yamma.

Shi kuwa Mike Adenuga hamshakin attajiri dan Nijeriya ya yi shuhura ne da Kamfaninsa na Globacom, kamfanin sadarwa na biyu mafi girma a Nijeriya wanda har ila yau yake da ressa a Ghana da Benin. Haka nan Mike yana da hannun jari a Bankin Ekuitorial Trust da kamfanin hakar mai na Conoil (wanda a da ake kira Consolidated Oil Company). Forbes ta kiyasta darajar arzikinsa ta kai dala biliyan 6.7 a 2024.

A bangaren Abdulsamad Rabiu, hamshakin attajirin kuma mai bayar da agaji kuwa, shi ne wanda ya kafa kuma yake shugabantar rukunin kamfanonin BUA Group, wadda ke maida hankali kan masana’antu, ababen more rayuwa, da noma da kuma samun kudaden shiga sama da dala biliyan 2.5.

Labarai Masu Nasaba

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Femi Otedola hamshakin dan kasuwa ne a Nijeriya wanda yake shugaban kamfanin Lantarki na Geregu Power Plc. Har ila yau, Otedola ne ya kafa Kamfanin mai na Zenon Petroleum and Gas Limited, kuma shi ne ya mallaki wasu kamfanoni da dama da suke hada-hadar jigilar kayayyaki, gidaje, da kudi. A baya-bayan nan ya zuba jari a fannin samar da wutar lantarki a wani bangare na ‘yantar da fannin a Nijeriya.

A cewar Forbes, shekara guda kenan da attajiran duniya, wadanda arzikinsu ke ci gaba da tabarbarewa yayin da kasuwannin hada-hadar hannayen jari na duniya ke cikin ka-ka-ni-ka-yi saboda rikicin siyasa, da hauhawar farashin kayayyaki.

“Kamar yadda yake a tsarin tattalin arziki gaba daya, an fi mayar da hankali ne wurin tattara bayanan kudi. Yanzu an sami jerin mutane 14 da ke cikin da’irar hamshakai da suka mallaki dala biliyan 100, da kuma wasu hamshakai da arzikinsu ya kai kirgen lambobi 12. Hakan ya kasance ne a kimanin shekara hudu da suka wuce. Wadannan suna daga cikin kalilan da suka taki sa’a, inda darajar arzikinsu ta kai dala tiriliyan 2 gaba daya, ma’ana kashi 0.5 cikin dari kacal na attajirai 2,781 na duniya da suka mallaki kashi 14 cikin dari na dukiyoyin attajiran da ke doron kasa”. In ji kafar a rahoton da ta fitar.

Kafar ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu an samu karin attajirai fiye da lokutan baya, inda ake da 2,781, an samu karin 141 idan aka kwatanta da yawansu a bara. Arzikinsu ya kai akalla dala tiriliyan 14.2 wanda aka samu karin dala tiriliyan 2 a kan na 2023.

Rahoton kafar ya kuma ayyana cewa Bernard Arnault shi ne ya ci gaba da rike kambunsa na hamshakin attajirin da ya fi kowa kudi a duniya. Attajirin mai kasuwancin kayan alatu dan kasar Faransa, an kiyasta yana da dala biliyan 233, inda ya samu karin dala biliyan 22 a kan abin da ya mallaka a 2023.

Amurka dai ita ce take da tarin hamshakan attajirai 813 wadanda arzikinsu ya kai dala tiriliyan 5.7, sai kasar Sin da take bi mata da yawan attajirai 473 da suka mallaki dala tiriliyan 1.7.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Dauki Matakin Da Ya Dace Bayan Bayyana Masu Daukar Nauyin Ta’addanci

Next Post

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

Related

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

10 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

11 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

11 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

13 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

14 hours ago
Next Post
kebbi

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.