• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar yada labarai ta Forbes ta bayyana sunayen wadanda suka zama attajirai mafiya arziki a Nijeriya a shekarar 2024. Su ne: Aliko Dangote, Mike Adenuga, Abdulsamad Rabiu, da Femi Otedola.

Kafar ta bayyana cewa Arzikin Dangote ya haura zuwa Dala biliyan 13.4, na Adenuga ya kai Dala biliyan 6.7, yayin da Abdulsalam Rabiu yake da Dala biliyan 5.2 shi kuma Otedola yake da dala biliyan 1.4.

  • Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya

Aliko Dangote shi ne mutumin da ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka kuma bakar fata mafi arziki a duniya, inda aka kiyasta kudinsa ya kai kusan dala biliyan 13.4 a shekarar 2024. Katafaren kasuwancinsa na rukunnan kamfanin Dangote Group, na daya daga cikin manyan kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya kuma kamfani mafi daraja a Afirka ta Yamma.

Shi kuwa Mike Adenuga hamshakin attajiri dan Nijeriya ya yi shuhura ne da Kamfaninsa na Globacom, kamfanin sadarwa na biyu mafi girma a Nijeriya wanda har ila yau yake da ressa a Ghana da Benin. Haka nan Mike yana da hannun jari a Bankin Ekuitorial Trust da kamfanin hakar mai na Conoil (wanda a da ake kira Consolidated Oil Company). Forbes ta kiyasta darajar arzikinsa ta kai dala biliyan 6.7 a 2024.

A bangaren Abdulsamad Rabiu, hamshakin attajirin kuma mai bayar da agaji kuwa, shi ne wanda ya kafa kuma yake shugabantar rukunin kamfanonin BUA Group, wadda ke maida hankali kan masana’antu, ababen more rayuwa, da noma da kuma samun kudaden shiga sama da dala biliyan 2.5.

Labarai Masu Nasaba

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Femi Otedola hamshakin dan kasuwa ne a Nijeriya wanda yake shugaban kamfanin Lantarki na Geregu Power Plc. Har ila yau, Otedola ne ya kafa Kamfanin mai na Zenon Petroleum and Gas Limited, kuma shi ne ya mallaki wasu kamfanoni da dama da suke hada-hadar jigilar kayayyaki, gidaje, da kudi. A baya-bayan nan ya zuba jari a fannin samar da wutar lantarki a wani bangare na ‘yantar da fannin a Nijeriya.

A cewar Forbes, shekara guda kenan da attajiran duniya, wadanda arzikinsu ke ci gaba da tabarbarewa yayin da kasuwannin hada-hadar hannayen jari na duniya ke cikin ka-ka-ni-ka-yi saboda rikicin siyasa, da hauhawar farashin kayayyaki.

“Kamar yadda yake a tsarin tattalin arziki gaba daya, an fi mayar da hankali ne wurin tattara bayanan kudi. Yanzu an sami jerin mutane 14 da ke cikin da’irar hamshakai da suka mallaki dala biliyan 100, da kuma wasu hamshakai da arzikinsu ya kai kirgen lambobi 12. Hakan ya kasance ne a kimanin shekara hudu da suka wuce. Wadannan suna daga cikin kalilan da suka taki sa’a, inda darajar arzikinsu ta kai dala tiriliyan 2 gaba daya, ma’ana kashi 0.5 cikin dari kacal na attajirai 2,781 na duniya da suka mallaki kashi 14 cikin dari na dukiyoyin attajiran da ke doron kasa”. In ji kafar a rahoton da ta fitar.

Kafar ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu an samu karin attajirai fiye da lokutan baya, inda ake da 2,781, an samu karin 141 idan aka kwatanta da yawansu a bara. Arzikinsu ya kai akalla dala tiriliyan 14.2 wanda aka samu karin dala tiriliyan 2 a kan na 2023.

Rahoton kafar ya kuma ayyana cewa Bernard Arnault shi ne ya ci gaba da rike kambunsa na hamshakin attajirin da ya fi kowa kudi a duniya. Attajirin mai kasuwancin kayan alatu dan kasar Faransa, an kiyasta yana da dala biliyan 233, inda ya samu karin dala biliyan 22 a kan abin da ya mallaka a 2023.

Amurka dai ita ce take da tarin hamshakan attajirai 813 wadanda arzikinsu ya kai dala tiriliyan 5.7, sai kasar Sin da take bi mata da yawan attajirai 473 da suka mallaki dala tiriliyan 1.7.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Dauki Matakin Da Ya Dace Bayan Bayyana Masu Daukar Nauyin Ta’addanci

Next Post

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

Related

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

48 minutes ago
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

9 hours ago
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025
Labarai

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

10 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Labarai

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

11 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

13 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

15 hours ago
Next Post
kebbi

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

LABARAI MASU NASABA

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.