• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Filato Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Tuhuma Da Laifin Safarar Kananan Yara

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Jihar Filato Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Tuhuma Da Laifin Safarar Kananan Yara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Filato ta bayyana aniyarta ta gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kananan hukumomi 17 na jihar inda take zargin lauyoyi da malaman addini da asibitoci da hannu a safarar yara a jihar.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Caroline Panglang Dafur ce ta bayyana hakan a lokacin da take kaddamar da ofishin kungiyar kare hakkin yara na jiha a Jos.

  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki
  • CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

Ta koka da yadda masu fataucin yara ke tafiya cikin hanzari a jihar, inda ta jaddada cewa a baya-bayan nan gwamnati ta gano wasu kararraki da dama.

A cewar kwamishinan, duk da kokarin da gwamnati ke yi na kawar da cin zarafin kananan yara a jihar, wasu marasa kishin kasa ciki har da masu fada a ji na kawo cikas a kokarinsu na shawo kan matsalar, yana mai jaddada cewa ya zama dole a hada karfi da karfe domin kawo karshen matsalar.

Ta ce, “Za mu gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kowace karamar hukuma daga cikin kananan hukumomi 17 na jihar. Na yi farin cikin kasancewa cikin wannan muhimmin lokaci. A halin yanzu, muna da mutane sama da 12 da ake tsare da su, kuma ina gayyatar ku da ku ziyarci wurin don shaida kokarin da muke yi. Wannan batu ya shafi ba kawai daidaikun mutane ba ne har ma da cibiyoyi kamar makarantu, asibitoci, har ma da masu aikin doka. Abin takaici, an samu wasu asibitoci da lauyoyi da masu fada a ji da hannu wajen safarar yara, wanda hakan bai dace ba.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

“Muna so mu yi gargadi ga dukanmu a nan. Wasu mutane na iya shiga cikin rashin sani a fataucin yara, suna ganin suna taimakon yara. Amma kafin ka sani, za ka iya samun kanka a cikin matsala ta shari’a. Dole ne mu kasance a fadake da kuma sanar da mu. Gwamnati ta kuduri aniyar kawar da duk wani mai hannu a wannan aika-aika, ba tare da la’akari da matsayinsa ko matsayinsa ba. Wannan gwamnati tana daukar yaki da fataucin yara da muhimmanci, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci cikakken nauyin doka.”

Da take jawabi tun da farko, Ko’odinetan CPN ta jihar, Misis Sandra Chikan, ta bayyana cewa akwai yawaitar cin zarafin yara, da sauran munanan dabi’u da ake musu, don haka akwai bukatar hada hannu da gwamnatin jihar domin magance wadannan matsaloli.

Ta ce, “Wannan shi ne lokacin da za mu kara daura damara. Lokaci ya yi da za mu hada kai, dmoni tunkarar matsalolin da suka shafi yaranmu. Ba za mu iya kara samun damar yin aiki a kebe ba Madadin haka, dole ne mu yi aiki a matsayin hadin kai, hadin gwiwa, gamayyar runduna masu azama.

“Abin takaicin da ke gabanmu shi ne yadda a kullum ake safarar yara marasa adadi a Jihar Filato. A wasu kananan hukumomi a jihar, ana zargin wasu yaran da bokaye, ana cin zarafinsu, kuma a lokuta masu tsanani, ana binne su ko a kashe su. Ba za a amince da wadannan ayyukan ba, ”in ji kodinetan jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu

Next Post

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

LABARAI MASU NASABA

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.