ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Filato Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Tuhuma Da Laifin Safarar Kananan Yara

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
11 months ago
Filato

Gwamnatin Jihar Filato ta bayyana aniyarta ta gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kananan hukumomi 17 na jihar inda take zargin lauyoyi da malaman addini da asibitoci da hannu a safarar yara a jihar.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Caroline Panglang Dafur ce ta bayyana hakan a lokacin da take kaddamar da ofishin kungiyar kare hakkin yara na jiha a Jos.

  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki
  • CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

Ta koka da yadda masu fataucin yara ke tafiya cikin hanzari a jihar, inda ta jaddada cewa a baya-bayan nan gwamnati ta gano wasu kararraki da dama.

ADVERTISEMENT

A cewar kwamishinan, duk da kokarin da gwamnati ke yi na kawar da cin zarafin kananan yara a jihar, wasu marasa kishin kasa ciki har da masu fada a ji na kawo cikas a kokarinsu na shawo kan matsalar, yana mai jaddada cewa ya zama dole a hada karfi da karfe domin kawo karshen matsalar.

Ta ce, “Za mu gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kowace karamar hukuma daga cikin kananan hukumomi 17 na jihar. Na yi farin cikin kasancewa cikin wannan muhimmin lokaci. A halin yanzu, muna da mutane sama da 12 da ake tsare da su, kuma ina gayyatar ku da ku ziyarci wurin don shaida kokarin da muke yi. Wannan batu ya shafi ba kawai daidaikun mutane ba ne har ma da cibiyoyi kamar makarantu, asibitoci, har ma da masu aikin doka. Abin takaici, an samu wasu asibitoci da lauyoyi da masu fada a ji da hannu wajen safarar yara, wanda hakan bai dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

“Muna so mu yi gargadi ga dukanmu a nan. Wasu mutane na iya shiga cikin rashin sani a fataucin yara, suna ganin suna taimakon yara. Amma kafin ka sani, za ka iya samun kanka a cikin matsala ta shari’a. Dole ne mu kasance a fadake da kuma sanar da mu. Gwamnati ta kuduri aniyar kawar da duk wani mai hannu a wannan aika-aika, ba tare da la’akari da matsayinsa ko matsayinsa ba. Wannan gwamnati tana daukar yaki da fataucin yara da muhimmanci, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci cikakken nauyin doka.”

Da take jawabi tun da farko, Ko’odinetan CPN ta jihar, Misis Sandra Chikan, ta bayyana cewa akwai yawaitar cin zarafin yara, da sauran munanan dabi’u da ake musu, don haka akwai bukatar hada hannu da gwamnatin jihar domin magance wadannan matsaloli.

Ta ce, “Wannan shi ne lokacin da za mu kara daura damara. Lokaci ya yi da za mu hada kai, dmoni tunkarar matsalolin da suka shafi yaranmu. Ba za mu iya kara samun damar yin aiki a kebe ba Madadin haka, dole ne mu yi aiki a matsayin hadin kai, hadin gwiwa, gamayyar runduna masu azama.

“Abin takaicin da ke gabanmu shi ne yadda a kullum ake safarar yara marasa adadi a Jihar Filato. A wasu kananan hukumomi a jihar, ana zargin wasu yaran da bokaye, ana cin zarafinsu, kuma a lokuta masu tsanani, ana binne su ko a kashe su. Ba za a amince da wadannan ayyukan ba, ”in ji kodinetan jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Next Post
Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.