ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Filato Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Tuhuma Da Laifin Safarar Kananan Yara

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Filato

Gwamnatin Jihar Filato ta bayyana aniyarta ta gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kananan hukumomi 17 na jihar inda take zargin lauyoyi da malaman addini da asibitoci da hannu a safarar yara a jihar.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Caroline Panglang Dafur ce ta bayyana hakan a lokacin da take kaddamar da ofishin kungiyar kare hakkin yara na jiha a Jos.

  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki
  • CBN Zai Ci Tarar Bankuna Naira Miliyan 150 Da Aka Kama Suna Sayar Da Sabbin Takardun Naira

Ta koka da yadda masu fataucin yara ke tafiya cikin hanzari a jihar, inda ta jaddada cewa a baya-bayan nan gwamnati ta gano wasu kararraki da dama.

ADVERTISEMENT

A cewar kwamishinan, duk da kokarin da gwamnati ke yi na kawar da cin zarafin kananan yara a jihar, wasu marasa kishin kasa ciki har da masu fada a ji na kawo cikas a kokarinsu na shawo kan matsalar, yana mai jaddada cewa ya zama dole a hada karfi da karfe domin kawo karshen matsalar.

Ta ce, “Za mu gurfanar da duk wanda aka samu da laifin safarar yara a kowace karamar hukuma daga cikin kananan hukumomi 17 na jihar. Na yi farin cikin kasancewa cikin wannan muhimmin lokaci. A halin yanzu, muna da mutane sama da 12 da ake tsare da su, kuma ina gayyatar ku da ku ziyarci wurin don shaida kokarin da muke yi. Wannan batu ya shafi ba kawai daidaikun mutane ba ne har ma da cibiyoyi kamar makarantu, asibitoci, har ma da masu aikin doka. Abin takaici, an samu wasu asibitoci da lauyoyi da masu fada a ji da hannu wajen safarar yara, wanda hakan bai dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

“Muna so mu yi gargadi ga dukanmu a nan. Wasu mutane na iya shiga cikin rashin sani a fataucin yara, suna ganin suna taimakon yara. Amma kafin ka sani, za ka iya samun kanka a cikin matsala ta shari’a. Dole ne mu kasance a fadake da kuma sanar da mu. Gwamnati ta kuduri aniyar kawar da duk wani mai hannu a wannan aika-aika, ba tare da la’akari da matsayinsa ko matsayinsa ba. Wannan gwamnati tana daukar yaki da fataucin yara da muhimmanci, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci cikakken nauyin doka.”

Da take jawabi tun da farko, Ko’odinetan CPN ta jihar, Misis Sandra Chikan, ta bayyana cewa akwai yawaitar cin zarafin yara, da sauran munanan dabi’u da ake musu, don haka akwai bukatar hada hannu da gwamnatin jihar domin magance wadannan matsaloli.

Ta ce, “Wannan shi ne lokacin da za mu kara daura damara. Lokaci ya yi da za mu hada kai, dmoni tunkarar matsalolin da suka shafi yaranmu. Ba za mu iya kara samun damar yin aiki a kebe ba Madadin haka, dole ne mu yi aiki a matsayin hadin kai, hadin gwiwa, gamayyar runduna masu azama.

“Abin takaicin da ke gabanmu shi ne yadda a kullum ake safarar yara marasa adadi a Jihar Filato. A wasu kananan hukumomi a jihar, ana zargin wasu yaran da bokaye, ana cin zarafinsu, kuma a lokuta masu tsanani, ana binne su ko a kashe su. Ba za a amince da wadannan ayyukan ba, ”in ji kodinetan jihar.

Filato
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Filato
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.