• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Zamfara Ce Kan Gaba Wajen Tattara Kuɗaɗen Shiga A Shekarar 2024 – Rahoto

by Leadership Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Jihar Zamfara Ce Kan Gaba Wajen Tattara Kuɗaɗen Shiga A Shekarar 2024 – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An sanya Jihar Zamfara a matsayin jihar da ke kan gaba a cikin Ayyukan Tattara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida a Nijeriya (IGR).

 

A wani rahoton wata ƙungiya mai bibiyar harkokin kasafin kuɗi da ake kira BudgIT na 2024, wanda aka ƙaddamar a makon da ya gabata a ranar Talata, bugu ne na shekara-shekara da ke kimanta ayyukan kasafin kuɗin kowace jiha na dogon lokaci da kuma ɗorewar kasafin kuɗin.

  • Kotu Ta Soke Tuhumar Da Ake Yi Wa Yaran Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Yinwa
  • Ƙungiyar Likitoci Ta Buƙaci Dakatar Da Kwamishina Kan Zargin Cin Zarafin Likita A Kano

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa babban ci gaban da aka samu wajen bunƙasar kuɗaɗen shiga na jihar Zamfara da kashi 240.44% na da nasaba da matakin da jihar ta ɗauka na cewa ba wai kawai ta dogara ne kocokan kan kason kuɗin da take samu daga ga Gwamnatin Tarayya (FAAC) ba ne.

Zamfara
Sakamakon rahoton kungiyar

Sanarwar ta ƙara da cewa, rahoton na BudgIT ya samu ne ta hanyar nazari da tantancewa da kuma ƙididdigar ayyukan kasafin kuɗi na dukkan jihohi 36, daga mafi yawa zuwa mafi ƙaranci.

Labarai Masu Nasaba

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

 

Rahoton na BudgIT ya bayyana gagarumin ci gaban da ake samu a jihar Zamfara ta hanyar tattara kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR), inda ya nuna cewa daga jiha ta 36 a shekarar 2023, Zamfara ta kai matsayi na 26 a shekarar 2024.

 

“Wannan gagarumin aikin za a iya danganta shi da yunƙurowar jihar bayan da ta samu koma baya na kashi 49.75 cikin 100 na IGR na shekarar 2022, inda ta ƙara da kashi 240.22% daga biliyan N6.51 a shekarar 2022 zuwa biliyan N22.16 a shekarar 2023.

 

“Ana samun ci gaban sosai a bangaren IGR na Zamfara duk shekara: Harajin ta na shiga ya ƙaru da kashi 142.26% daga biliyan N5.03 a 2022 zuwa biliyan N12.18, lasisi ya ƙaru da 5921.22% daga miliyan N22.78 a 2022 zuwa N1.37 Biliyan a 2023, Kuɗaɗen sun ƙaru da kashi 3610.38% daga miliyan N82.44 a 2022 zuwa biliyan N3.06 a 2023.

 

“Bugu da ƙari, tarar ta tashi da kashi 1924.52% daga miliyan N24.15 a 2022 zuwa miliyan N491.32 a 2023, ayyukan tallace-tallace ya ƙaru da kashi 32.49% daga miliyan N772.06 a 2022 zuwa biliyan N1.02 a 2023, abin da ake samu ya ƙaru da kashi 5.7% zuwa 582% a 2022 zuwa miliyan N562.48 a 2023, kuma abin da ake samu daga sauran haraji ya ƙaru da kashi 519.71% daga miliyan N412.03 a 2022 zuwa biliyan N2.55 a 2023.

 

“Bugu da ƙari kuma, jihar ta samu kuɗaɗen shiga daga hayar gine-ginen gwamnati, hayar filaye da sauran su da samun kaɗaɗe daga zuba hannun jari duk an shigar da su cikin kuɗaɗen shiga a shekarar da ta gabata. Zamfara za ta iya nuna aniyar inganta tattalin arzikinta ta hanyar binciko albarkatun ƙasa tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Tarayya don karkato da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

“Jimillar kuɗaɗen shigar jihar ya ƙaru da kashi 65.35% zuwa Naira Biliyan 144.95 a shekarar 2023 daga Naira Biliyan 87.68 da ta samu a shekarar da ta gabata. Dangane da tsarin kuɗaɗen shigar da ake samu akai-akai, alamun masu ƙarfi sun nuna cewa jihar na fuskantar raguwar samun kuɗaɗen shiga daga shekarar da ta gabata yayin da dogaro kacokan kan kason kuɗin da take samu daga Gwamnatin Tarayya daga kashi 90.52% a shekarar 2022 zuwa kashi 74.66% a shekarar 2023, duk da rabon kuɗin da kashi 4.93% daga biliyan N62.21 zuwa biliyan N65.28. A ƙarshe, Ayyukan Tattara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida a Nijeriya (IGR) zuwa rabon kuɗaɗen shiga na yau da kullum na 2023 ya kasance kashi 22.16% sama da kashi 9.48% a cikin 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Next Post

Xi Ya Bukaci A Gina Rundunar Sojin Sama Mai Karfi Kuma Na Zamani

Related

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

32 minutes ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

1 hour ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

3 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

5 hours ago
Borno
Labarai

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

7 hours ago
Yajin aiki
Labarai

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

8 hours ago
Next Post
Xi Ya Bukaci A Gina Rundunar Sojin Sama Mai Karfi Kuma Na Zamani

Xi Ya Bukaci A Gina Rundunar Sojin Sama Mai Karfi Kuma Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.