• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai koyar da tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, Jose Peseiro ya shafe watanni shida yana aiki ba tare da an biya shi albashi ba kamar yadda rahotanni suka bayyana wanda hakan wani koma-baya ne.

Kocin mai shekara 62 wanda ya soma aiki tun a watan Mayu bai fito fili ya gabatar da korafinsa ba game da hukumar kwallon kafa ta Nijeriya kan kin biyansa albashinsa, sai dai a martanin da hukumar kwallon kafa ta kasa ta mayar, ta bayyana cewa ta soma samar da tsare-tsare kan yadda za ta biya basussukan da ake binta.

  • Kasar Sin Za Ta Kafa Karin Yankunan Misali 29 Na Inganta Shigo Da Kayayyaki Kasar
  • Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa

Kamar yadda yake, dama dai akwai wadanda ke bin wannan hukumar kudi kamar tsohon mai koyar da tawagar wato Gernot Rohr wanda shi ne ya gabaci Peseiro da kuma wasu ‘yan wasan na Nijeriya

Wakilin mai koyarwa Peseiro ya bayyana cewa alawus-alawus dinsa kadai ya karba wanda a hakan abin damuwa ne saboda haka akwai bukatar kamar yadda wani ma’aikacin hukumar kwallon kafar ya shaida.

A ka’ida dai ma’aikatar wasanni ce ke biyan albashin mai koyarwa, amma sun yi sauri sun fito da wani sabon tsari da hadin kan ma’aikatar domin warware batun albashin a wannan makon da ake ciki.

Labarai Masu Nasaba

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Ma’ikatar wasanni ta kasa wadda ita ke da alhakkin biyan Peseiro ta dora laifin kan tsaiko da aka samu daga gwamnatin tarayya wurin samun kudin, kuma wani mai bayar da shawara ga ministan wasanni na kasar Sunday Dare ya tabbatar da cewa za a biya kocin ba da dadewa ba

Sai dai daman ba wannan ne karon farko ba da ake korafin kin biyan kocin kwallon kafa albashinsu a kan kari ba, domin akwai masu horar da kungiyar kwallon kafan Nijeriya da dama da har suka bar aiki suna bin bashi ba tare da an biya su ba.

Daga cikinsu akwai Christian Chukwu da Augustine Eguaboen da Samson Siasia da Sunday Oliseh da Florence Omagbemi da marigayi Shaibu Amodu kuma marigayi Stephen Keshi, kuma har yanzu dai Rohr yana bin NFF kudi. Haka kuma akwai ‘yan wasan Nijeriya maza da mata da ke bin hukumar kudi.

Dan wasan Super Eagles ba su ji dadi dangane da kin biyansu garabasa da kuma alawus dinsu na tun shekarar 2021 ba. Haka kuma ita ma kungyiar Super Falcons na jiran NFF da ma’aikatar wasanni su biya su bashin da suke bi na gasar kwallon kafa ta mata ta Afrika wato Wafcon.

Ko a watan Yuli sai da ‘yan wasan Nijeriya mata suka kaurace wa atisaye kafin su buga wasan da suka zama na uku a gasar WAFCON saboda kin biyansu alawus dinsu da ya kamata a biya su tun lokacin da aka kammala gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaAlbashiBashiKociNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani

Next Post

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Related

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
Wasanni

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

4 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

19 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

1 day ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

LABARAI MASU NASABA

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.