• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai koyar da tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, Jose Peseiro ya shafe watanni shida yana aiki ba tare da an biya shi albashi ba kamar yadda rahotanni suka bayyana wanda hakan wani koma-baya ne.

Kocin mai shekara 62 wanda ya soma aiki tun a watan Mayu bai fito fili ya gabatar da korafinsa ba game da hukumar kwallon kafa ta Nijeriya kan kin biyansa albashinsa, sai dai a martanin da hukumar kwallon kafa ta kasa ta mayar, ta bayyana cewa ta soma samar da tsare-tsare kan yadda za ta biya basussukan da ake binta.

  • Kasar Sin Za Ta Kafa Karin Yankunan Misali 29 Na Inganta Shigo Da Kayayyaki Kasar
  • Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa

Kamar yadda yake, dama dai akwai wadanda ke bin wannan hukumar kudi kamar tsohon mai koyar da tawagar wato Gernot Rohr wanda shi ne ya gabaci Peseiro da kuma wasu ‘yan wasan na Nijeriya

Wakilin mai koyarwa Peseiro ya bayyana cewa alawus-alawus dinsa kadai ya karba wanda a hakan abin damuwa ne saboda haka akwai bukatar kamar yadda wani ma’aikacin hukumar kwallon kafar ya shaida.

A ka’ida dai ma’aikatar wasanni ce ke biyan albashin mai koyarwa, amma sun yi sauri sun fito da wani sabon tsari da hadin kan ma’aikatar domin warware batun albashin a wannan makon da ake ciki.

Labarai Masu Nasaba

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Ma’ikatar wasanni ta kasa wadda ita ke da alhakkin biyan Peseiro ta dora laifin kan tsaiko da aka samu daga gwamnatin tarayya wurin samun kudin, kuma wani mai bayar da shawara ga ministan wasanni na kasar Sunday Dare ya tabbatar da cewa za a biya kocin ba da dadewa ba

Sai dai daman ba wannan ne karon farko ba da ake korafin kin biyan kocin kwallon kafa albashinsu a kan kari ba, domin akwai masu horar da kungiyar kwallon kafan Nijeriya da dama da har suka bar aiki suna bin bashi ba tare da an biya su ba.

Daga cikinsu akwai Christian Chukwu da Augustine Eguaboen da Samson Siasia da Sunday Oliseh da Florence Omagbemi da marigayi Shaibu Amodu kuma marigayi Stephen Keshi, kuma har yanzu dai Rohr yana bin NFF kudi. Haka kuma akwai ‘yan wasan Nijeriya maza da mata da ke bin hukumar kudi.

Dan wasan Super Eagles ba su ji dadi dangane da kin biyansu garabasa da kuma alawus dinsu na tun shekarar 2021 ba. Haka kuma ita ma kungyiar Super Falcons na jiran NFF da ma’aikatar wasanni su biya su bashin da suke bi na gasar kwallon kafa ta mata ta Afrika wato Wafcon.

Ko a watan Yuli sai da ‘yan wasan Nijeriya mata suka kaurace wa atisaye kafin su buga wasan da suka zama na uku a gasar WAFCON saboda kin biyansu alawus dinsu da ya kamata a biya su tun lokacin da aka kammala gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaAlbashiBashiKociNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani

Next Post

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Related

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
Wasanni

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

3 days ago
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Wasanni

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

4 days ago
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

4 days ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

4 days ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

6 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

1 week ago
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.