• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai koyar da tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, Jose Peseiro ya shafe watanni shida yana aiki ba tare da an biya shi albashi ba kamar yadda rahotanni suka bayyana wanda hakan wani koma-baya ne.

Kocin mai shekara 62 wanda ya soma aiki tun a watan Mayu bai fito fili ya gabatar da korafinsa ba game da hukumar kwallon kafa ta Nijeriya kan kin biyansa albashinsa, sai dai a martanin da hukumar kwallon kafa ta kasa ta mayar, ta bayyana cewa ta soma samar da tsare-tsare kan yadda za ta biya basussukan da ake binta.

  • Kasar Sin Za Ta Kafa Karin Yankunan Misali 29 Na Inganta Shigo Da Kayayyaki Kasar
  • Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa

Kamar yadda yake, dama dai akwai wadanda ke bin wannan hukumar kudi kamar tsohon mai koyar da tawagar wato Gernot Rohr wanda shi ne ya gabaci Peseiro da kuma wasu ‘yan wasan na Nijeriya

Wakilin mai koyarwa Peseiro ya bayyana cewa alawus-alawus dinsa kadai ya karba wanda a hakan abin damuwa ne saboda haka akwai bukatar kamar yadda wani ma’aikacin hukumar kwallon kafar ya shaida.

A ka’ida dai ma’aikatar wasanni ce ke biyan albashin mai koyarwa, amma sun yi sauri sun fito da wani sabon tsari da hadin kan ma’aikatar domin warware batun albashin a wannan makon da ake ciki.

Labarai Masu Nasaba

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Ma’ikatar wasanni ta kasa wadda ita ke da alhakkin biyan Peseiro ta dora laifin kan tsaiko da aka samu daga gwamnatin tarayya wurin samun kudin, kuma wani mai bayar da shawara ga ministan wasanni na kasar Sunday Dare ya tabbatar da cewa za a biya kocin ba da dadewa ba

Sai dai daman ba wannan ne karon farko ba da ake korafin kin biyan kocin kwallon kafa albashinsu a kan kari ba, domin akwai masu horar da kungiyar kwallon kafan Nijeriya da dama da har suka bar aiki suna bin bashi ba tare da an biya su ba.

Daga cikinsu akwai Christian Chukwu da Augustine Eguaboen da Samson Siasia da Sunday Oliseh da Florence Omagbemi da marigayi Shaibu Amodu kuma marigayi Stephen Keshi, kuma har yanzu dai Rohr yana bin NFF kudi. Haka kuma akwai ‘yan wasan Nijeriya maza da mata da ke bin hukumar kudi.

Dan wasan Super Eagles ba su ji dadi dangane da kin biyansu garabasa da kuma alawus dinsu na tun shekarar 2021 ba. Haka kuma ita ma kungyiar Super Falcons na jiran NFF da ma’aikatar wasanni su biya su bashin da suke bi na gasar kwallon kafa ta mata ta Afrika wato Wafcon.

Ko a watan Yuli sai da ‘yan wasan Nijeriya mata suka kaurace wa atisaye kafin su buga wasan da suka zama na uku a gasar WAFCON saboda kin biyansu alawus dinsu da ya kamata a biya su tun lokacin da aka kammala gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaAlbashiBashiKociNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kayan Makulashen Hausawa Na Zamani

Next Post

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Related

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

5 hours ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

1 day ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

2 days ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

3 days ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

5 days ago
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.