ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jose Peseiro Yana Bin Nijeriya Albashin Wata Shida

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Nijeriya

Mai koyar da tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, Jose Peseiro ya shafe watanni shida yana aiki ba tare da an biya shi albashi ba kamar yadda rahotanni suka bayyana wanda hakan wani koma-baya ne.

Kocin mai shekara 62 wanda ya soma aiki tun a watan Mayu bai fito fili ya gabatar da korafinsa ba game da hukumar kwallon kafa ta Nijeriya kan kin biyansa albashinsa, sai dai a martanin da hukumar kwallon kafa ta kasa ta mayar, ta bayyana cewa ta soma samar da tsare-tsare kan yadda za ta biya basussukan da ake binta.

  • Kasar Sin Za Ta Kafa Karin Yankunan Misali 29 Na Inganta Shigo Da Kayayyaki Kasar
  • Manoman Alkama 200 Za Su Amfana Da Shirin NALDA A Jihar Jigawa

Kamar yadda yake, dama dai akwai wadanda ke bin wannan hukumar kudi kamar tsohon mai koyar da tawagar wato Gernot Rohr wanda shi ne ya gabaci Peseiro da kuma wasu ‘yan wasan na Nijeriya

ADVERTISEMENT

Wakilin mai koyarwa Peseiro ya bayyana cewa alawus-alawus dinsa kadai ya karba wanda a hakan abin damuwa ne saboda haka akwai bukatar kamar yadda wani ma’aikacin hukumar kwallon kafar ya shaida.

A ka’ida dai ma’aikatar wasanni ce ke biyan albashin mai koyarwa, amma sun yi sauri sun fito da wani sabon tsari da hadin kan ma’aikatar domin warware batun albashin a wannan makon da ake ciki.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Ma’ikatar wasanni ta kasa wadda ita ke da alhakkin biyan Peseiro ta dora laifin kan tsaiko da aka samu daga gwamnatin tarayya wurin samun kudin, kuma wani mai bayar da shawara ga ministan wasanni na kasar Sunday Dare ya tabbatar da cewa za a biya kocin ba da dadewa ba

Sai dai daman ba wannan ne karon farko ba da ake korafin kin biyan kocin kwallon kafa albashinsu a kan kari ba, domin akwai masu horar da kungiyar kwallon kafan Nijeriya da dama da har suka bar aiki suna bin bashi ba tare da an biya su ba.

Daga cikinsu akwai Christian Chukwu da Augustine Eguaboen da Samson Siasia da Sunday Oliseh da Florence Omagbemi da marigayi Shaibu Amodu kuma marigayi Stephen Keshi, kuma har yanzu dai Rohr yana bin NFF kudi. Haka kuma akwai ‘yan wasan Nijeriya maza da mata da ke bin hukumar kudi.

Dan wasan Super Eagles ba su ji dadi dangane da kin biyansu garabasa da kuma alawus dinsu na tun shekarar 2021 ba. Haka kuma ita ma kungyiar Super Falcons na jiran NFF da ma’aikatar wasanni su biya su bashin da suke bi na gasar kwallon kafa ta mata ta Afrika wato Wafcon.

Ko a watan Yuli sai da ‘yan wasan Nijeriya mata suka kaurace wa atisaye kafin su buga wasan da suka zama na uku a gasar WAFCON saboda kin biyansu alawus dinsu da ya kamata a biya su tun lokacin da aka kammala gasar.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Yadda FIFA Ta Yi Yunƙurin Sasanta Rikicin Israila Da Amurka A Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.