• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: Kasashen Burkina, Guinea Da Mali Sun Yi Barazanar Taimakawa Nijar Kan Yaki Da ECOWAS

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Juyin Mulki: Kasashen Burkina, Guinea Da Mali Sun Yi Barazanar Taimakawa Nijar Kan Yaki Da ECOWAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen Mali, Burkina Faso, da Guinea, da ke yammacin Afirka, sun goyi bayan juyin mulki a Nijar, lamarin da ke barazana ga zaman lafiyar yankin.

 

Juyin mulkin da aka yi a Burkina Faso da Mali a baya-bayan nan dai ya samo asali ne sakamakon takaicin yadda hukumomi suka gaza shawo kan ‘yan ta’adda masu ikirarin kishin addinin Musulunci da ke addabar yankin wanda ya hada da kasar Nijar.

  • Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Bayan da aka shafe kusan sa’o’i 48 ba a san halin da ake ciki ba a Niamey, babban birnin Nijar, Abdourahamane Tiani, wani janar kuma tsohon maigadin fadar shugaban kasa, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasa.

 

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

A wani zama na musamman da kungiyar ECOWAS ta gudanar a ranar Lahadin da ta gabata, karkashin jagorancin shugabanta Bola Tinubu a Abuja, an cimma matsayar sanyawa Nijar takunkumi da dama kan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar.

 

ECOWAS ta kuma ba da wa’adin mako guda ga sojojin da suka yi juyin mulkin da su mika mulki ga zababbiyar gwamnatin Bazoum.

 

Ya zuwa yanzu, sojojin sun yi watsi da kiraye-kiraye da dama daga wasu kasashe da kungiyoyin duniya na maido da Bazoum matsayin shugaban kasar.

 

Kasashe irinsu Amurka da Jamus da kungiyoyi irin su Tarayyar Turai sun dakatar da tallafin kudi da suke baiwa Nijar sabida Allah wadai da juyin mulkin.

 

Wani bangare na kudurin ECOWAS a ranar Lahadin da ta gabata, shi ne na yin amfani da dukkan matakan da suka dace wajen maido da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar, ciki har da yin amfani da karfin soji idan ba a biya mata bukatunta nan da mako guda ba.

 

A cikin wata sanarwar hadin guiwa da kasashen Mali, Burkina suka fitar a ranar Litinin, sun gargadi ECOWAS game da duk wani matakin da zai kawo cikas ga zaman lafiyar yankin.

 

Kasashen sun yi gargadi cewa, amfani da karfin soji a kan Nijar zai tilasta musu su ma su dauki matakan kare kai domin tallafa wa dakarun Nijar da kuma al’ummar Nijar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cire Tallafin Man Fetur: Nijeriya Za Ta Farfado Nan Gaba Kadan – Inji Gwamnan Gombe

Next Post

Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

Related

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa
Labarai

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

9 hours ago
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

13 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

14 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

16 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

19 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

20 hours ago
Next Post
Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.