• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: Kasashen Burkina, Guinea Da Mali Sun Yi Barazanar Taimakawa Nijar Kan Yaki Da ECOWAS

by Sulaiman
2 years ago
Juyin mulki

Kasashen Mali, Burkina Faso, da Guinea, da ke yammacin Afirka, sun goyi bayan juyin mulki a Nijar, lamarin da ke barazana ga zaman lafiyar yankin.

 

Juyin mulkin da aka yi a Burkina Faso da Mali a baya-bayan nan dai ya samo asali ne sakamakon takaicin yadda hukumomi suka gaza shawo kan ‘yan ta’adda masu ikirarin kishin addinin Musulunci da ke addabar yankin wanda ya hada da kasar Nijar.

  • Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Bayan da aka shafe kusan sa’o’i 48 ba a san halin da ake ciki ba a Niamey, babban birnin Nijar, Abdourahamane Tiani, wani janar kuma tsohon maigadin fadar shugaban kasa, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

A wani zama na musamman da kungiyar ECOWAS ta gudanar a ranar Lahadin da ta gabata, karkashin jagorancin shugabanta Bola Tinubu a Abuja, an cimma matsayar sanyawa Nijar takunkumi da dama kan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar.

 

ECOWAS ta kuma ba da wa’adin mako guda ga sojojin da suka yi juyin mulkin da su mika mulki ga zababbiyar gwamnatin Bazoum.

 

Ya zuwa yanzu, sojojin sun yi watsi da kiraye-kiraye da dama daga wasu kasashe da kungiyoyin duniya na maido da Bazoum matsayin shugaban kasar.

 

Kasashe irinsu Amurka da Jamus da kungiyoyi irin su Tarayyar Turai sun dakatar da tallafin kudi da suke baiwa Nijar sabida Allah wadai da juyin mulkin.

 

Wani bangare na kudurin ECOWAS a ranar Lahadin da ta gabata, shi ne na yin amfani da dukkan matakan da suka dace wajen maido da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar, ciki har da yin amfani da karfin soji idan ba a biya mata bukatunta nan da mako guda ba.

 

A cikin wata sanarwar hadin guiwa da kasashen Mali, Burkina suka fitar a ranar Litinin, sun gargadi ECOWAS game da duk wani matakin da zai kawo cikas ga zaman lafiyar yankin.

 

Kasashen sun yi gargadi cewa, amfani da karfin soji a kan Nijar zai tilasta musu su ma su dauki matakan kare kai domin tallafa wa dakarun Nijar da kuma al’ummar Nijar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.