ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: Kasashen Burkina, Guinea Da Mali Sun Yi Barazanar Taimakawa Nijar Kan Yaki Da ECOWAS

by Sulaiman
3 years ago
Juyin mulki

Kasashen Mali, Burkina Faso, da Guinea, da ke yammacin Afirka, sun goyi bayan juyin mulki a Nijar, lamarin da ke barazana ga zaman lafiyar yankin.

 

Juyin mulkin da aka yi a Burkina Faso da Mali a baya-bayan nan dai ya samo asali ne sakamakon takaicin yadda hukumomi suka gaza shawo kan ‘yan ta’adda masu ikirarin kishin addinin Musulunci da ke addabar yankin wanda ya hada da kasar Nijar.

ADVERTISEMENT
  • Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Bayan da aka shafe kusan sa’o’i 48 ba a san halin da ake ciki ba a Niamey, babban birnin Nijar, Abdourahamane Tiani, wani janar kuma tsohon maigadin fadar shugaban kasa, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

A wani zama na musamman da kungiyar ECOWAS ta gudanar a ranar Lahadin da ta gabata, karkashin jagorancin shugabanta Bola Tinubu a Abuja, an cimma matsayar sanyawa Nijar takunkumi da dama kan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar.

 

ECOWAS ta kuma ba da wa’adin mako guda ga sojojin da suka yi juyin mulkin da su mika mulki ga zababbiyar gwamnatin Bazoum.

 

Ya zuwa yanzu, sojojin sun yi watsi da kiraye-kiraye da dama daga wasu kasashe da kungiyoyin duniya na maido da Bazoum matsayin shugaban kasar.

 

Kasashe irinsu Amurka da Jamus da kungiyoyi irin su Tarayyar Turai sun dakatar da tallafin kudi da suke baiwa Nijar sabida Allah wadai da juyin mulkin.

 

Wani bangare na kudurin ECOWAS a ranar Lahadin da ta gabata, shi ne na yin amfani da dukkan matakan da suka dace wajen maido da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar, ciki har da yin amfani da karfin soji idan ba a biya mata bukatunta nan da mako guda ba.

 

A cikin wata sanarwar hadin guiwa da kasashen Mali, Burkina suka fitar a ranar Litinin, sun gargadi ECOWAS game da duk wani matakin da zai kawo cikas ga zaman lafiyar yankin.

 

Kasashen sun yi gargadi cewa, amfani da karfin soji a kan Nijar zai tilasta musu su ma su dauki matakan kare kai domin tallafa wa dakarun Nijar da kuma al’ummar Nijar.

Juyin mulki
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • Sulaiman
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
Labarai

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Next Post
Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

Da Dumi-dumi: Abdullahi Gwarzo Zai Maye Gurbin Ganduje A Matsayin Minista Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.