• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Manyan Kafafen Labarai Ke Fuskanta A Yanzu – Shugaban MacArthur

by Idris Umar
1 year ago
in Tattaunawa
0
Kalubalen Da Manyan Kafafen Labarai Ke Fuskanta A Yanzu – Shugaban MacArthur
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne, Shugaban Gidauniyar ‘MacArthur Foundation’ KOLE SHATIMA, ya zanta da wakilinmu IDRIS UMAR ZARIYA a kan halin da gidajen jaridu suke ciki da su kansu ‘yan jaridar tare da tsokaci a kan ayyukan gidauniyar mai ofisoshi a Chikago ta Amurka, da Delhin Indiya da kuma Abujar Nijeriya. Ga yadda ta kasance:

Masu karatu za su so jin shin da wa suke tare a daidai wannan lokaci?

Sunana Kole Shatima, ni ne kuma Shugaban ‘MacArthur Foundation’, mai ofis a Chicago da Kasar Indiya da kuma nan Abuja Nijeriya.

Wadane irin ayyuka wannan gidauniya da ka ke shugabanta ta ke yi wa al’umma?

Gidauniyar ‘MacArthur Foundation’, tana bayar da gudummawa a bangarori da dama, musamman a bangaren yada labarai, wato gidajen jaridu, Talabijin har ma da Rediyo; muna ba su tallafi, domin su rika fitar da rahotanni ko labarai masu inganci, wanda zai wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

A jerin gidajen yada labarai, wanda wannan gidauniya ta bai wa ire-iren wannan tallafi, akwai kamar BBC, Daily Trust, Arewa 24 da sauran makamantansu. Har ila yau, misali ka ga yanzu haka ana gudanar da babban taro na kasa a nan Jami’ar Ahmadu Bello, wanda ganin muhimmancin taron ne ya sa muka shigo, domin bayar da gudunmawarmu, sakamakon gabatar da taron da za a yi a kan yada labarai cikin tsaro a zamanin da muke ciki na ci gaban rayuwa.

Yaushe kuka fara wannan kokari na tallafa wa kafafen yada labarai, sannan wane sakamako kuke bukata?

To gaskiya mun kai shekara takwas da farawa, sannan kuma daga cikin bukatun da muke nema su ne: Da yake yanzu komai ya canza, gidajen jaridu babu wata riba da suke samu sakamakon ci gaban da ake samu na zamani, misali da yawan masu amfani da yanar gizo (social media) wajen aiwatar da tallace-tallacen hajarsu, sun fi masu manyan kamfanonin gidajen jaridu samun kudin shiga.

Wannan dalili ne ya sa muka ce in har ba a so gidajen jaridu su yada rahotannin karya, wato rahoton da zai tayar da hankali, wajibi ne a taimaka musu; domin kuwa hakan ne zai kare su daga yada rahotannin da ba na gaskiya ba. Ma’ana, bayar da tallafi ne zai sa a sanya rahoto mai inganci, wanda mu kuma hakan shi ne muradunmu, shi muke so ya tabbata a koda-yaushe.

Har ila yau dalilinmu shi ne, idan aka bar gidajen jaridu babu wani mai taimakon su a irin matsalar rashin kudin shiga da ake fama da shi yanzu, ko shakka babu mahukunta za su iya amfani da wannan dama su saye gidajen, domin buga musu irin abin da suke so; wanda hakan ko kadan bai dace ba.

Me ya kamata a yi a irin wannan hali da ake ciki?

Gaskiya abin da ya kamata a yi shi ne, taimakon gidajen jaridu tare da bai wa su kansu ‘yan jarida kulawa ta musamman wajen gudanar da ayyukansu. Hakan ne zai sa a rika tantance rahotanin da aka samu kafin a watsa su ga daukacin al’umma.

Wane kira za ka yi ga su kansu ‘yan jarida masu zuwa neman rahotanni a cikin  l’umma babu dare ba rana?

Kiran da zan yi ga ‘yan jarida shi ne, don Allah kafin su saki kowane irin labari, su tabbata sun tantance shi yadda ya kamata, don gudun tayar da fitina a cikin al’umma; ma’ana dai su rika jin dukkanin bangarori biyu kafin su kai ga watsa shi.

Sannan, idan ya zama dole sai an saki labara; to a tabbatar da cewa an fadi gaskiya, ka da a fadi karya. Abu na biyu kuma da zan bai wa ‘yan jarida shawara a kai shi ne, su guji sanya banbancin addini a yayin gudanar da ayyukansu, domin kuwa aikin jarida bai gaji haka ba ko kadan.

A karshe, wace shawara za ka bai wa gwamnati kan yadda ‘yan jarida ke gudanar da ayyukansu a nan Nijeriya?

A nan, shawarata ga gwamnati ita ce, ya kamata ta rika sanar da ‘yan jarida halin da take ciki, hakan zai taimaka wajen fitar da rahotannin gaskya. Abu na biyu kuma shi ne, ya kamata gwamnati ta kula da hakkin ‘yan jarida komai kankantansa, domin kuwa hakan zai taimaka wajen samar da labarai masu inganci a cikin al’umma, domin su ma ‘yan jaridar suna da ‘yanci cikakke ba bayi ba ne.

Ko kana da wani abin cewa wanda ban taMbaye ka ba?

Kwarai kuwa akwai shi, ina so na yi amfani da wannan dama, don yin jinjina ga sashen koyar da ilmin yada labarai na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, (Mass Communication Department) da shugaban sojoji; Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, bisa yadda ya bayar da gudunmawarsa da kuma mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambassada Ahmed Nuhu Bamalli da Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Kabir Bala da daluban sashin koyar da aikin jarida da kuma dukkanin ma’aikatanmu na ‘MacArthur Foundation’ da suka halarci wannan taro na karawa juna sani, a kan kalubalen da ake fuskanta a bangaren yada labarai a sashin tsaro tare da neman mafita mai inganci.

Haka zalika, na ji dadi matuka da gudunmawar da gidauniyar tamu ta bayar; muna alfari da hakan kwarai da gaske tare da fatan za a ci gaba da samun irin sa a tsakanin al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Yadda Za A Yi Mutum Ya Yi Rubutu Ba Tare Da Allah Ya Ba Shi Baiwa Ba –Khadija

Next Post

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (3)

Related

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya
Tattaunawa

Ma’aikatar Kasuwanci Da Zuba Jari Ta Gudanar Da Bikin Makon Abokan Cinikayya

7 months ago
Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u
Tattaunawa

Yadda Na Juya Jarin Naira 15,000 Zuwa Babbar Harka – Safara’u

7 months ago
Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
Tattaunawa

Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka

9 months ago
Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris
Tattaunawa

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

9 months ago
Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina
Tattaunawa

Rashin Amfani Da Ilimin Taurari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki – Sheikh Muhajjadina

10 months ago
Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa
Tattaunawa

Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

10 months ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (3)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (3)

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.