ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Manyan Kafafen Labarai Ke Fuskanta A Yanzu – Shugaban MacArthur

by Idris Umar
2 years ago
Labarai

A makon da ya gabata ne, Shugaban Gidauniyar ‘MacArthur Foundation’ KOLE SHATIMA, ya zanta da wakilinmu IDRIS UMAR ZARIYA a kan halin da gidajen jaridu suke ciki da su kansu ‘yan jaridar tare da tsokaci a kan ayyukan gidauniyar mai ofisoshi a Chikago ta Amurka, da Delhin Indiya da kuma Abujar Nijeriya. Ga yadda ta kasance:

Masu karatu za su so jin shin da wa suke tare a daidai wannan lokaci?

Sunana Kole Shatima, ni ne kuma Shugaban ‘MacArthur Foundation’, mai ofis a Chicago da Kasar Indiya da kuma nan Abuja Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Wadane irin ayyuka wannan gidauniya da ka ke shugabanta ta ke yi wa al’umma?

Gidauniyar ‘MacArthur Foundation’, tana bayar da gudummawa a bangarori da dama, musamman a bangaren yada labarai, wato gidajen jaridu, Talabijin har ma da Rediyo; muna ba su tallafi, domin su rika fitar da rahotanni ko labarai masu inganci, wanda zai wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

A jerin gidajen yada labarai, wanda wannan gidauniya ta bai wa ire-iren wannan tallafi, akwai kamar BBC, Daily Trust, Arewa 24 da sauran makamantansu. Har ila yau, misali ka ga yanzu haka ana gudanar da babban taro na kasa a nan Jami’ar Ahmadu Bello, wanda ganin muhimmancin taron ne ya sa muka shigo, domin bayar da gudunmawarmu, sakamakon gabatar da taron da za a yi a kan yada labarai cikin tsaro a zamanin da muke ciki na ci gaban rayuwa.

Yaushe kuka fara wannan kokari na tallafa wa kafafen yada labarai, sannan wane sakamako kuke bukata?

To gaskiya mun kai shekara takwas da farawa, sannan kuma daga cikin bukatun da muke nema su ne: Da yake yanzu komai ya canza, gidajen jaridu babu wata riba da suke samu sakamakon ci gaban da ake samu na zamani, misali da yawan masu amfani da yanar gizo (social media) wajen aiwatar da tallace-tallacen hajarsu, sun fi masu manyan kamfanonin gidajen jaridu samun kudin shiga.

Wannan dalili ne ya sa muka ce in har ba a so gidajen jaridu su yada rahotannin karya, wato rahoton da zai tayar da hankali, wajibi ne a taimaka musu; domin kuwa hakan ne zai kare su daga yada rahotannin da ba na gaskiya ba. Ma’ana, bayar da tallafi ne zai sa a sanya rahoto mai inganci, wanda mu kuma hakan shi ne muradunmu, shi muke so ya tabbata a koda-yaushe.

Har ila yau dalilinmu shi ne, idan aka bar gidajen jaridu babu wani mai taimakon su a irin matsalar rashin kudin shiga da ake fama da shi yanzu, ko shakka babu mahukunta za su iya amfani da wannan dama su saye gidajen, domin buga musu irin abin da suke so; wanda hakan ko kadan bai dace ba.

Me ya kamata a yi a irin wannan hali da ake ciki?

Gaskiya abin da ya kamata a yi shi ne, taimakon gidajen jaridu tare da bai wa su kansu ‘yan jarida kulawa ta musamman wajen gudanar da ayyukansu. Hakan ne zai sa a rika tantance rahotanin da aka samu kafin a watsa su ga daukacin al’umma.

Wane kira za ka yi ga su kansu ‘yan jarida masu zuwa neman rahotanni a cikin  l’umma babu dare ba rana?

Kiran da zan yi ga ‘yan jarida shi ne, don Allah kafin su saki kowane irin labari, su tabbata sun tantance shi yadda ya kamata, don gudun tayar da fitina a cikin al’umma; ma’ana dai su rika jin dukkanin bangarori biyu kafin su kai ga watsa shi.

Sannan, idan ya zama dole sai an saki labara; to a tabbatar da cewa an fadi gaskiya, ka da a fadi karya. Abu na biyu kuma da zan bai wa ‘yan jarida shawara a kai shi ne, su guji sanya banbancin addini a yayin gudanar da ayyukansu, domin kuwa aikin jarida bai gaji haka ba ko kadan.

A karshe, wace shawara za ka bai wa gwamnati kan yadda ‘yan jarida ke gudanar da ayyukansu a nan Nijeriya?

A nan, shawarata ga gwamnati ita ce, ya kamata ta rika sanar da ‘yan jarida halin da take ciki, hakan zai taimaka wajen fitar da rahotannin gaskya. Abu na biyu kuma shi ne, ya kamata gwamnati ta kula da hakkin ‘yan jarida komai kankantansa, domin kuwa hakan zai taimaka wajen samar da labarai masu inganci a cikin al’umma, domin su ma ‘yan jaridar suna da ‘yanci cikakke ba bayi ba ne.

Ko kana da wani abin cewa wanda ban taMbaye ka ba?

Kwarai kuwa akwai shi, ina so na yi amfani da wannan dama, don yin jinjina ga sashen koyar da ilmin yada labarai na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, (Mass Communication Department) da shugaban sojoji; Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, bisa yadda ya bayar da gudunmawarsa da kuma mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambassada Ahmed Nuhu Bamalli da Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Kabir Bala da daluban sashin koyar da aikin jarida da kuma dukkanin ma’aikatanmu na ‘MacArthur Foundation’ da suka halarci wannan taro na karawa juna sani, a kan kalubalen da ake fuskanta a bangaren yada labarai a sashin tsaro tare da neman mafita mai inganci.

Haka zalika, na ji dadi matuka da gudunmawar da gidauniyar tamu ta bayar; muna alfari da hakan kwarai da gaske tare da fatan za a ci gaba da samun irin sa a tsakanin al’umma.

Labarai
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattaunawa

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

July 11, 2026
Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu
Tattaunawa

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

April 10, 2026
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Tattaunawa

Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

April 4, 2026
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (3)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (3)

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.