• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Tsaro: Gwamnatin Zamfara Na Shirin Kafa Sabuwar Hukumar Tsaro Ta (CPG)

by Muhammad
3 years ago
Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamnatin Jihar Zamfara na ci gaba da tsarin kyautata tsaron cikin gida, ta hangar kafa sabuwar hukumar tsaro da zata yi aiki wajen dakile yawaitar kashe-kashe da ‘yan fashin daji a jihar.

Kalubalen
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Sabuwar hukumar tsaron wanda ake kira ‘Community Protection Guards (CPG)’ kwatankwacin kungiyar tsaro ta Yammacin Nijeriya, wacce aka fi sani da Amotekun, wacce ta fara aiki a watan Janairun 2020.

  • ‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato
  • A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

An fara horar da kashin farko na mutum 500, wadanda aka dauka daga dukkan masarautu 19 da ke jihar.

Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamna Bello Matawalle ya kaddamar da horon a ranar Asabar a Gusau.

Matawalle ya ce gwamnatin jihar Zamfara ta fara daukar sabbin matakan tsaro, ya ce masu Jami’a za su dauki makamai yayin gabatar da aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Gwamnan ya ce, an yanke shawarar kafa jami’an kare hakkin jama’ar ne saboda burin gwamnatinsa na samar da duk hanyoyin da za a bi don magance karuwar ayyukan ‘yan fashi da ke haddasa asarar rayuka da wahalhalun da ba a taba gani ba da kuma wargaza zaman lafiya a wasu sassan jihar.

Matawalle ya shaidawa Jami’an Tsaron Al’uma aikin da ke gabansu, sannan ya bukace su da su mayar da hankali sosai kan horar da suke samu.

Matawalle ya tabbatar da cewa, a karshen wannan horon, za a tura mambobin CPG zuwa yankunansu daban-daban na masarautun jihar 19, domin baiwa jami’an tsaro kwarin gwiwa wajen yaki da ‘yan fashi da miyagun laifuka.

Elkana yayin da yake bayyana cikakken goyon bayan rundunar ga Gwamna Matawalle a yakin da ake yi da ‘yan fashi, ya bukaci masu daukar ma’aikata da su kasance masu bin doka da oda, masu tsoron Allah, kuma masu kishin kasa wajen gudanar da ayyukansu domin cimma burin da ake so.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Rtd DIG Mamman Ibrahim Tsafe ya ce an kafa jami’an kare hakkin jama’a ne da nufin taimakawa jami’an tsaro wajen ganin an tabbatar da tsaro a jihar daga dukkan munanan laifuka a duk sassan jihar.

Taron ya samu halartar shugaban majalisar dokokin jihar Zamfara, Nasiru Muazu Magarya da sakataren gwamnatin jiha Alhaji Kabiru Balarabe.

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar Gusau, Malam Ibrahim Suleiman, shugaban ma’aikata na jiha, Alhaji Kabiru Muhammad Gayari, ‘yan majalisar zartarwa na jiha da shugabannin hukumomin tsaro da ke aiki a jihar, suma sun halarci taron kaddamar da shirin horaswar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din ‘Izzar So’ Nura Mustapha Waye, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din 'Izzar So' Nura Mustapha Waye, Rasuwa

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.