ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Tsaro: Gwamnatin Zamfara Na Shirin Kafa Sabuwar Hukumar Tsaro Ta (CPG)

by Muhammad
4 years ago
Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamnatin Jihar Zamfara na ci gaba da tsarin kyautata tsaron cikin gida, ta hangar kafa sabuwar hukumar tsaro da zata yi aiki wajen dakile yawaitar kashe-kashe da ‘yan fashin daji a jihar.

Kalubalen
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Sabuwar hukumar tsaron wanda ake kira ‘Community Protection Guards (CPG)’ kwatankwacin kungiyar tsaro ta Yammacin Nijeriya, wacce aka fi sani da Amotekun, wacce ta fara aiki a watan Janairun 2020.

  • ‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato
  • A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

An fara horar da kashin farko na mutum 500, wadanda aka dauka daga dukkan masarautu 19 da ke jihar.

ADVERTISEMENT
Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamna Bello Matawalle ya kaddamar da horon a ranar Asabar a Gusau.

Matawalle ya ce gwamnatin jihar Zamfara ta fara daukar sabbin matakan tsaro, ya ce masu Jami’a za su dauki makamai yayin gabatar da aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Gwamnan ya ce, an yanke shawarar kafa jami’an kare hakkin jama’ar ne saboda burin gwamnatinsa na samar da duk hanyoyin da za a bi don magance karuwar ayyukan ‘yan fashi da ke haddasa asarar rayuka da wahalhalun da ba a taba gani ba da kuma wargaza zaman lafiya a wasu sassan jihar.

Matawalle ya shaidawa Jami’an Tsaron Al’uma aikin da ke gabansu, sannan ya bukace su da su mayar da hankali sosai kan horar da suke samu.

Matawalle ya tabbatar da cewa, a karshen wannan horon, za a tura mambobin CPG zuwa yankunansu daban-daban na masarautun jihar 19, domin baiwa jami’an tsaro kwarin gwiwa wajen yaki da ‘yan fashi da miyagun laifuka.

Elkana yayin da yake bayyana cikakken goyon bayan rundunar ga Gwamna Matawalle a yakin da ake yi da ‘yan fashi, ya bukaci masu daukar ma’aikata da su kasance masu bin doka da oda, masu tsoron Allah, kuma masu kishin kasa wajen gudanar da ayyukansu domin cimma burin da ake so.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Rtd DIG Mamman Ibrahim Tsafe ya ce an kafa jami’an kare hakkin jama’a ne da nufin taimakawa jami’an tsaro wajen ganin an tabbatar da tsaro a jihar daga dukkan munanan laifuka a duk sassan jihar.

Taron ya samu halartar shugaban majalisar dokokin jihar Zamfara, Nasiru Muazu Magarya da sakataren gwamnatin jiha Alhaji Kabiru Balarabe.

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar Gusau, Malam Ibrahim Suleiman, shugaban ma’aikata na jiha, Alhaji Kabiru Muhammad Gayari, ‘yan majalisar zartarwa na jiha da shugabannin hukumomin tsaro da ke aiki a jihar, suma sun halarci taron kaddamar da shirin horaswar.

Kalubalen
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din ‘Izzar So’ Nura Mustapha Waye, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din 'Izzar So' Nura Mustapha Waye, Rasuwa

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.