ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Tsaro: Gwamnatin Zamfara Na Shirin Kafa Sabuwar Hukumar Tsaro Ta (CPG)

by Muhammad
4 years ago
Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamnatin Jihar Zamfara na ci gaba da tsarin kyautata tsaron cikin gida, ta hangar kafa sabuwar hukumar tsaro da zata yi aiki wajen dakile yawaitar kashe-kashe da ‘yan fashin daji a jihar.

Kalubalen
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Sabuwar hukumar tsaron wanda ake kira ‘Community Protection Guards (CPG)’ kwatankwacin kungiyar tsaro ta Yammacin Nijeriya, wacce aka fi sani da Amotekun, wacce ta fara aiki a watan Janairun 2020.

  • ‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato
  • A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

An fara horar da kashin farko na mutum 500, wadanda aka dauka daga dukkan masarautu 19 da ke jihar.

ADVERTISEMENT
Jami'an Tsaron Zamfara Ta JTF
Jami’an Tsaron Zamfara Ta JTF

Gwamna Bello Matawalle ya kaddamar da horon a ranar Asabar a Gusau.

Matawalle ya ce gwamnatin jihar Zamfara ta fara daukar sabbin matakan tsaro, ya ce masu Jami’a za su dauki makamai yayin gabatar da aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Gwamnan ya ce, an yanke shawarar kafa jami’an kare hakkin jama’ar ne saboda burin gwamnatinsa na samar da duk hanyoyin da za a bi don magance karuwar ayyukan ‘yan fashi da ke haddasa asarar rayuka da wahalhalun da ba a taba gani ba da kuma wargaza zaman lafiya a wasu sassan jihar.

Matawalle ya shaidawa Jami’an Tsaron Al’uma aikin da ke gabansu, sannan ya bukace su da su mayar da hankali sosai kan horar da suke samu.

Matawalle ya tabbatar da cewa, a karshen wannan horon, za a tura mambobin CPG zuwa yankunansu daban-daban na masarautun jihar 19, domin baiwa jami’an tsaro kwarin gwiwa wajen yaki da ‘yan fashi da miyagun laifuka.

Elkana yayin da yake bayyana cikakken goyon bayan rundunar ga Gwamna Matawalle a yakin da ake yi da ‘yan fashi, ya bukaci masu daukar ma’aikata da su kasance masu bin doka da oda, masu tsoron Allah, kuma masu kishin kasa wajen gudanar da ayyukansu domin cimma burin da ake so.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida Rtd DIG Mamman Ibrahim Tsafe ya ce an kafa jami’an kare hakkin jama’a ne da nufin taimakawa jami’an tsaro wajen ganin an tabbatar da tsaro a jihar daga dukkan munanan laifuka a duk sassan jihar.

Taron ya samu halartar shugaban majalisar dokokin jihar Zamfara, Nasiru Muazu Magarya da sakataren gwamnatin jiha Alhaji Kabiru Balarabe.

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar Gusau, Malam Ibrahim Suleiman, shugaban ma’aikata na jiha, Alhaji Kabiru Muhammad Gayari, ‘yan majalisar zartarwa na jiha da shugabannin hukumomin tsaro da ke aiki a jihar, suma sun halarci taron kaddamar da shirin horaswar.

Kalubalen
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din ‘Izzar So’ Nura Mustapha Waye, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Daraktan fim Din 'Izzar So' Nura Mustapha Waye, Rasuwa

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.