ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum na jihar Zamfara, Suleiman Abubakar Gumi, ya ce ‘Yan bindiga sun tashi sama da garuruwa 30 a cikin wannan watan na Yuni.

by Muhammad
4 years ago
'Yan

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum na jihar Zamfara, Suleiman Abubakar Gumi, ya ce ‘Yan bindiga sun tashi sama da garuruwa 30 a cikin wannan watan na Yuni.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da kudiri kan bukatar sojoji su tura karin dakaru zuwa yankunan da abin ya shafa a jihar domin dakile hare-haren da ke kara ta’azzara.

  • Gwamnan Zamfara Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kisa Ga Masu Kai Wa ‘Yan Bindiga Rahoto 
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matar Shugaban NULGE Reshen Zamfara Mai Dauke Da Juna Biyu

Gumi ya ce a baya-bayan nan, ‘yan bindiga sun kai hari a wasu yankunan jihar, inda suka kashe mutane 16, suka jikkata wasu da dama, sun yi awon gaba da shanu da lalata dukiyoyi tare da kona ofisoshin ‘yan sanda da kuma abinci.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, babu wata rana da za ta wuce ba tare da kai hari a yankin ba.

Ya ce mazauna kauyuka kusan 71 sun bar gidajensu; yayin da manoma suka yi watsi da gonakinsu domin tsira.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya ce ‘yan fashin sun sanya haraji kan al’ummar yankin tare da neman kudin fansa daga wadanda suka yi garkuwa da su.

Hakazalika, ‘yan bindiga sun bayar da sanarwar barin kauyukan Sabon Zama, Gindin Dutse, Anguwan Tsohon Soja, Anguwar Yuhana da Anguwan Mangu da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato.

Pinau, wani ƙauye mai nisan kilomita 11 daga Wase, ƙauyukan sun kewaye shi.

Mazauna yankin sun ce wasu ‘yan bindiga da suka rufe fuska sun afkawa mutanen yankin, inda suka bukaci ko dai su fice nan da kwanaki biyar ko kuma su fuskanci tashin hankali.

Ubale Pinau, wani mazaunin garin Pinau, ya shaida cewa ‘yan bindigar sun yi barazanar kai hari a yankin, inda ya shawarce su da su fice idan ba haka ba su fuskanci abin da zai biyo baya.

Ya ce mutane da dama sun fara tururuwa zuwa Pinau da sauran manyan garuruwa domin tsira.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Ishaku Takwa, ya ce bai san da sanarwar sallamar ba.

'Yan
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato

'Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.