ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamala Harris Na Ci Gaba Da Samun Goyon Bayan Takara A Democrat

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Mataimakiyar Shugaban Amurka, Kamala Harris ta samu goyon baya mai rinjaye na wakilan jam’iyyar Democrat domin kasancewa ‘yar takarar shugabancin kasar a jam’iyyar.

Wani bincike da kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya yi ya nuna cewa Kamala ta samu goyon baya daga wakilan jami’iyyar fiye da 1,976 da take bukata ta samu nasarar zama ‘yar takarar jam’iyyar a zagayen farko na zaben.

  • Za A Ci Gaba Da Daukar Shirin ‘The Mandate’ A Kasar Faransa – Ezinne Agwu
  • Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa’o’i 2 A Amurka

Hakan kuwa na nufin Misis Harris na dab da zama ‘yar takarar shugabancin kasar ta jam’iyyar ta Democrat domin karawa da dan takarar jam’iyyar Republican, Donald Trump a babban zaben na watan Nuwamba.

ADVERTISEMENT

Sai dai hakan zai zama a hukumance ne kawai lokacin da wakilan jam’iyyar da za su zaben suka kada kuri’a a babban taron jam’iyyar a Chikago a wata mai kamawa.

Wakilan dai su ne mutanen da ke wakiltar mazabunsu. Kuma alkawarin goyon bayan da suka sanar bai zama wajibi su bi ba har sai lokacin kada kuri’a duk da dai da wuya hakan ya sauya.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

har yanzu dai babu wani da ya fito a bayyane ya kalubalanci Misis Harris tun bayan da shugaba Joe Biden ya sanar da ficewa daga takarar ranar Lahadi.

Ya fuskanci matsin lamba daga jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sakamakon rashin katabus a mahawarar da ya yi da Mista Trump.

Idan dai har irin goyon bayan da take samu zai zama kuri’a a lokacin taron jam’iyyar Democrat da za a yi tsakanin ranar 1 zuwa 7 ga watan Agustan 2024, to Misis Harris za ta zamo ‘yar takarar jam’iyyar.

Binciken na AP na nuni da irin girman goyon bayan da Kamala Harris ke samu tun bayan da Joe Biden ya sanar da ajiye takarar tasa.

Har wayau wani abu shi ne yadda aka tara wa Kamala Harris tallafin miliyoyin Daloli tun bayan sanarwar ficewar ta Mista Biden sanna kuma jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sun shirya goya mata baya.

Ana sa ran Misis Harris za ta bayyana a wani gangamin magoya baya a Milwaukee da ke Jihar Winsconsin ranar Talata kuma wanda shi ne zai zama gangaminta na farko tun bayan da Mista Biden ya fice daga takarar kuma ya goyi bayan mataimakiyar tasa.

A wani bangaren kuma Mista Biden zai koma fadar White House bayan kwashe dan wani lokaci sakamakon kamuwa da cutar Korona. Mista Biden zai gana da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu a wannan makon a yayin ziyarar da Netanyahun zai kai Washinton.

Da take jawabi ga ma’aikata a ofishin kamfe dinta a Wimington a Jihar Delaware Misis Harris alamu sun nuna ta shirya wa Mista Trump.

Da take bayyana kanta a matsayin mai shari’ar da ta hukunta masu laifi, sai ta kara da cewa: “Na san irin su Donald Trump.”

Ta kara da cewa takarar Biden da Harris ta zamo wani da ke alamta kishin makomar Amurka da tasu da kuma ta Donald Trump.

“Wani yana duba gaba, dayan kuma yana waiwayen baya,” Harris ta ce. “Donald Trump yana son komar da kasarmu baya mu kuma mun yi imani da makoma mai kyau da za ta yi kyau ga dukkannin Amurkawa.”

Ta kuma yi nuni da irin nasarorin da Mista Biden ya samu, tana mai cewa aikin da ta yi tare da shi a matsayinta na mataimakiyar shugaban kasa “shi ne wani abun da cimma babba a rayuwarta”.

kafin dai Misis Harris ta hau dandamalin kmafe ta fara magana, sai da mista Biden ya fara yin tsokaci ta wayar tarho a wani yanayi na farko tun bayan sanarwar da ya yi na ficewa daga takarar bayan kamuwa da cutar korona.

Ya fara ne da yin godiya ga masu taimaka masa inda ya nemi da su “rungumi” Misis Harris saboda “ita ce ta fi dacewa”.

“Na san cewa labarin da kuka ji jiya ya girgiza ku to sai dai abin da ya fi dacewa a yi kenan,” In ji Mista Biden.

Ya kuma sha lawashin shiga gangamin nema mata kuri’a kan-jiki-kankarfi kasancewar yadda mulkin demokradiyya ke fuskantar barazana.

Shi kuma mataimakin Donald Trumpna jam’iyyar Republican, Sanata JD Bance, ya soki Misis Harris da Mista Biden baki dayansu a lokacin yakin neman zabe a Birginia.

“Tarihi zai rinka tuna wa da Joe Biden ba kawai a matsayin dan takarar da ya gudu ya bar ladansa ba, har ma da kasancewarsa shugaban Amurka da ya fi kowane lalacewa,” in ji shi.

Kamala
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Firaministan Vanuatu: Tunanin Al’ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

Firaministan Vanuatu: Tunanin Al'ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.