ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamala Harris Na Ci Gaba Da Samun Goyon Bayan Takara A Democrat

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Mataimakiyar Shugaban Amurka, Kamala Harris ta samu goyon baya mai rinjaye na wakilan jam’iyyar Democrat domin kasancewa ‘yar takarar shugabancin kasar a jam’iyyar.

Wani bincike da kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya yi ya nuna cewa Kamala ta samu goyon baya daga wakilan jami’iyyar fiye da 1,976 da take bukata ta samu nasarar zama ‘yar takarar jam’iyyar a zagayen farko na zaben.

  • Za A Ci Gaba Da Daukar Shirin ‘The Mandate’ A Kasar Faransa – Ezinne Agwu
  • Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa’o’i 2 A Amurka

Hakan kuwa na nufin Misis Harris na dab da zama ‘yar takarar shugabancin kasar ta jam’iyyar ta Democrat domin karawa da dan takarar jam’iyyar Republican, Donald Trump a babban zaben na watan Nuwamba.

ADVERTISEMENT

Sai dai hakan zai zama a hukumance ne kawai lokacin da wakilan jam’iyyar da za su zaben suka kada kuri’a a babban taron jam’iyyar a Chikago a wata mai kamawa.

Wakilan dai su ne mutanen da ke wakiltar mazabunsu. Kuma alkawarin goyon bayan da suka sanar bai zama wajibi su bi ba har sai lokacin kada kuri’a duk da dai da wuya hakan ya sauya.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

har yanzu dai babu wani da ya fito a bayyane ya kalubalanci Misis Harris tun bayan da shugaba Joe Biden ya sanar da ficewa daga takarar ranar Lahadi.

Ya fuskanci matsin lamba daga jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sakamakon rashin katabus a mahawarar da ya yi da Mista Trump.

Idan dai har irin goyon bayan da take samu zai zama kuri’a a lokacin taron jam’iyyar Democrat da za a yi tsakanin ranar 1 zuwa 7 ga watan Agustan 2024, to Misis Harris za ta zamo ‘yar takarar jam’iyyar.

Binciken na AP na nuni da irin girman goyon bayan da Kamala Harris ke samu tun bayan da Joe Biden ya sanar da ajiye takarar tasa.

Har wayau wani abu shi ne yadda aka tara wa Kamala Harris tallafin miliyoyin Daloli tun bayan sanarwar ficewar ta Mista Biden sanna kuma jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sun shirya goya mata baya.

Ana sa ran Misis Harris za ta bayyana a wani gangamin magoya baya a Milwaukee da ke Jihar Winsconsin ranar Talata kuma wanda shi ne zai zama gangaminta na farko tun bayan da Mista Biden ya fice daga takarar kuma ya goyi bayan mataimakiyar tasa.

A wani bangaren kuma Mista Biden zai koma fadar White House bayan kwashe dan wani lokaci sakamakon kamuwa da cutar Korona. Mista Biden zai gana da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu a wannan makon a yayin ziyarar da Netanyahun zai kai Washinton.

Da take jawabi ga ma’aikata a ofishin kamfe dinta a Wimington a Jihar Delaware Misis Harris alamu sun nuna ta shirya wa Mista Trump.

Da take bayyana kanta a matsayin mai shari’ar da ta hukunta masu laifi, sai ta kara da cewa: “Na san irin su Donald Trump.”

Ta kara da cewa takarar Biden da Harris ta zamo wani da ke alamta kishin makomar Amurka da tasu da kuma ta Donald Trump.

“Wani yana duba gaba, dayan kuma yana waiwayen baya,” Harris ta ce. “Donald Trump yana son komar da kasarmu baya mu kuma mun yi imani da makoma mai kyau da za ta yi kyau ga dukkannin Amurkawa.”

Ta kuma yi nuni da irin nasarorin da Mista Biden ya samu, tana mai cewa aikin da ta yi tare da shi a matsayinta na mataimakiyar shugaban kasa “shi ne wani abun da cimma babba a rayuwarta”.

kafin dai Misis Harris ta hau dandamalin kmafe ta fara magana, sai da mista Biden ya fara yin tsokaci ta wayar tarho a wani yanayi na farko tun bayan sanarwar da ya yi na ficewa daga takarar bayan kamuwa da cutar korona.

Ya fara ne da yin godiya ga masu taimaka masa inda ya nemi da su “rungumi” Misis Harris saboda “ita ce ta fi dacewa”.

“Na san cewa labarin da kuka ji jiya ya girgiza ku to sai dai abin da ya fi dacewa a yi kenan,” In ji Mista Biden.

Ya kuma sha lawashin shiga gangamin nema mata kuri’a kan-jiki-kankarfi kasancewar yadda mulkin demokradiyya ke fuskantar barazana.

Shi kuma mataimakin Donald Trumpna jam’iyyar Republican, Sanata JD Bance, ya soki Misis Harris da Mista Biden baki dayansu a lokacin yakin neman zabe a Birginia.

“Tarihi zai rinka tuna wa da Joe Biden ba kawai a matsayin dan takarar da ya gudu ya bar ladansa ba, har ma da kasancewarsa shugaban Amurka da ya fi kowane lalacewa,” in ji shi.

Kamala
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Firaministan Vanuatu: Tunanin Al’ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

Firaministan Vanuatu: Tunanin Al'ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.