ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
12 months ago
Iran

Fafatawar yaki a tsakanin kasashen Iran da Isra’ila na ci-gaba da daukar hankalin al’ummar duniya bakidaya tare da sanya fargaba da zullumin yadda yakin zai zama kuma ya kasance. 

Masana na ganin yakin zai iya zama hadari da koma baya ga kasashe da dama ciki har da Nijeriya a daidai lokacin da tattalin arzikin duniya ke ci-gaba da tabarbarewa. 

  • Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Yakin da ake ci-gaba da gwabzawa tsakanin kasashen wanda ya girgiza duniya bakidaya zai iya shafar tattalin arzikin Nijeriya ta fuskoki da dama.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai Nijeriya kamar sauran kasashen Afurka tuni ta yi tir da matakin da Isra’ila ta dauka na kaiwa Iran hari ta na cewar hakan zai haifar da gagarumar matsalar da ba a san karshen illar ta ba. 

Gumurzun Iran da Isra’ila da aka fara a ranar 13 ga Yuni 2025, ya riga ya yi tasiri ga tattalin arzikin duniya wanda ya haifar da rashin tabbas, karin kudin albarkatun mai da cikas ga kasuwanci da fitar da kaya a kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya ci-gaban mai hakar rijiya ne ga Nijeriya wadda ke kan gaba wajen fitar da mai ta yadda za ta samu makuddan kudin shiga sai dai gagarumar matsala ce ga ‘yan kasa wadanda za su fuskanci karin mai a cikin gida wanda zai zama silar karin kunci a dalilin farashin abubuwa da dama da zai hau sama. 

A cewar masana, Gabas ta Tsakiya da ke samar da akalla kashi 34 na mai a duniya da kashi 18 na gas, gumurzun kasashen biyu ya haddasa farashin danyen mai tashi da kashi 10, yayin da gas ya kara da kashi 7. Haka ma akwai fargabar Isra’ila na iya illata harkokin mai da jigilarsa a mashigar Hormuz da ke karkashin ikon Iran.

Baya ga wannan farashin rarraba kaya da fitar da kaya ta jiragen ruwa ya karu a bisa ga tashin kudin inshoran jiragen ruwa a Gabas ta Tsakiya wanda ya kawo tsaikon kasuwanci a duniya. 

A yanzu haka dai a wannan makon kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) ya fitar da sanarwar karin kudin mai a gidajen man sa a fadin kasar bakidaya. 

Tun a kwanan baya masana suka bayyana cewar farashin man fetur zai tashi a kasuwannin duniya a dalilin fafatawar yakin Iran da Isra’ila. 

Kamfanin ya bayyana karin kudin mai zuwa naira 945 wanda karin ya biyo bayan karin kudin mai da matatar mai ta Dangote mai zaman kan ta ta yi zuwa naira 880. 

A bayyana yake cewar Iran babbar kasa ce daga cikin manyan kasashen duniya masu karfin arzikin man fetur da ke fitar da shi a kasashen duniya don haka wajibi ne yaki da kasar ya shafi tattalin arzikin kasashe da dama. 

Duk da matatar mai ta Dangote ta na aiki amma har zuwa yanzu shigo da man fetur ake yi a Nijeriya don haka tashin farashin a kasuwannin duniya na nufin tashin farashinsa a Nijeriya kamar yadda masana suka bayyana. 

Da yake bayani kan illar yakin ga Nijeriya, masani kan tattalin arziki da huldar diflomasiyya kuma Shehin Malami a jami’ar Ibadan, Farfesa Tayo Bello ya yi gargadin yakin zai shafi Nijeriya da babban kalubale sosai. 

Ya ce Nijeriya wadda ita ce babbar kasar Afurka mafi albarkatun mai za ta ci-gaba da amfana da karin kudin mai a gajeren lokaci, amma hakan zai haifar da gagarumar illa ga ‘yan Nijeriya a gida.

“Yakin tamkar takobi biyu ne mai kaifi ga Nijeriya, a daya hannu a na tsammanin farashin mai a kasuwar duniya zai tashi sosai. Hakan na nufin Nijeriya za ta ci-gaba da samun karin haraji sosai musamman idan farashin ya tashi daga dala 75 a ganga daya zuwa dala 90 ko sama da haka.”

“Karin kudin mai a duniya na nufin karin kudin mai a Nijeriya. Man dizel, fetur da sauran abubuwa za su yi tsada sosai wanda hakan na nufin hauhawar farashi sosai.”

Injiniya Yabagi Sani fitaccen mai sharhi kan al’ummarran man fetur a Nijeriya ya bayyanawa BBC Hausa cewar illar da yakin ya yi wa sauran kasashen duniya shine ya shafi Nijeriya. 

Ya ce a bayyane yake kusan kashi 20 zuwa 30 na mai da ake hada- hadarsa a kasuwannin duniya a na yin sa ne ta mashigar Hormuz da ke karkashin kasar Iran don haka su ke da ikon shiga da ficen mai. 

Masanin ya bayyana cewar a sakamakon wannan yakin Iran ta yi barazanar rufe mashigar wanda sakamakon fargabar matsalar da za ta iya biyowa baya, jiragen dakon man fetur suka fara kauracewa mashigar wanda a cewarsa wannan ne ya haifar da karancin mai a kasuwandnin duniya bakidaya.”  

Shi kuwa tsohon jakadan Nijeriya a kasar Ethiopia, Bulus Lolo na ganin ko kadan ba alheri ba ne ga kowa ciki har da Nijeriya kan ci-gaba da nunawa juna yatsa da kasashen biyu ke yi. 

Ya ce a wasu lokutan fada irin wannan yana da amfani, a wasu lokutan kuma ba ya da amfani. Nijeriya ba ta fuskantar farmaki kai tsaye, amma ta na amayar da muryar ta kan kasashen biyu da su tsagaita wuta su daina kaiwa juna hari, a zauna a teburin sulhu.*

Ya ce kasuwar mai a duniya za ta shaidi artabun da ke faruwa a ma’ajiyar man Iran, amma ba su fatar kazantar lamariin a  kasuwar duniya, a cewarsa suna fatar abubuwa za su daidaita domin hasashen su ya tafi daidai. 

“Akwai yiyuwar karin kudi ta yadda farashi zai hau sama sosai amma har zuwa yaushe? Sabani ne wanda ba mu san yadda karshensa zai kasance ba.” In ji Lolo. 

Masana da jama’a na ganin mafitar kawar da radadin farashin mai a Nijeriya shine gwamnafi ta inganta matatun mai, ta yadda za su rika aiki yadda ya kamata domin samar da wadataccen mai ga ‘yan kasa.

Haka ma gwamnati za ta iya saukakawa jama’a ta hanyar rage farashin mai wanda hakan zai magance hauhawar farashin kaya da al’umma ke fargaba a halin yanzu.

Iran
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.