ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Ci Gaba Da Daukar Shirin ‘The Mandate’ A Kasar Faransa – Ezinne Agwu

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
mandate

Masana’antar Nollywood tana gab da shaida wani gagarumin ci gaba, a yayin da Dakta Princess Ezinne Agwu, sabuwar mai shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, ta kammala shirin fim na farko na miliyoyin nairori mai suna, “The Mandate,” a birnin Paris na kasar Faransa.

Dakta Ezinne, wacce ta canza sana’a daga mai shari’a ta kasa da kasa zuwa harkar fim, ta hada kai da fitaccen daraktan Nollywood, Ike Nnaebue domin kawo wannan wasan kwaikwayo a idon duniya.

  • Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?
  • Ali Nuhu Ya Gabatar Da Lacca Kan Fina-finan Nijeriya A Faransa

Ike Nnaebue, wanda ya dawo harkar fina-finai na barkwanci bayan nasarar shirinsa na “No U-Turn,” shi ne darakta a wannan shiri wanda ake fatan idan an kammala shi ya zama irinsa na farko da wani dan Nijeriya ya taba shiryawa. Wannan fim din ya janyo wa Dakta Ezinne yabo mai yawa da suka hada da jinjinan ‘Jury Berlinale’ da kyaututtuka daga kwalejin fina-finan Afirka da bikin fina-finai na duniya na Durban.

ADVERTISEMENT

Da yake magana game da fin din “The Mandate” da hadin gwiwarsa tare da Dakta Ezinne, Ike ya ce wannan buri ne na kowane mai shirya fina-finai, domin yin aiki mai nagarta tare da samar da fasaha mai muhimmanci.

Ya ce fim din “The Mandate” labari ne na jarumtaka a cikin duniyar da tsoro ya zama aikin yau da kullun.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Majiyoyin da ke kusa da ‘Royalty Life Studios’, inda Dakta Ezinne ke aiki a matsayin shugaba, sun nuna cewa kasafin kudin fim din ya wuce naira miliyan 700.  Sai dai Dakta Ezinne ta ki tabbatar da ainihin alkaluman, inda ta ce, “Ba a gama fim din ba tukuna, za mu bayyana kasafin kudin fim din idan an kamala shi.

Labarin fim din ya nuna yadda Dakta Ezinne Egbuna, Darakta-Janar na Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, wanda ke kalubalantar halin da ake ciki a fagen siyasar Nijeriya da maza suka mamaye.

A yunkurinta na yaki da cin hanci da rashawa da bunkasar ci gaba, ta yi murabus daga mukaminta mai daraja ta tsaya takarar gwamna a karkashin jam’iyyar DPC, karkashin jagorancin Hon.  Lucas Amadi, wanda yake fuskantar adawa mai zafi daga DPA da makiya na boye a cikin jam’iyyar tasa.

Fim din ya kunshi fitattun jaruman da suka hada da Femi Adebayo, Deyemi Okanlawon, Ali Nuhu, Kalu Ikeagwu, Okey Bakasi, Sarauniya Dimma Edochie, Chioma Nwoha da kuma gabatar da sabon jarumi, Peter Ngene.

Dakta Ezinne ta jaddada cewa shawarar da aka yanke na gudanar da ayyukan bayan fage a birnin Paris ya yi daidai da hangen nesanta na samar da labarun gida tare da jawo hankalin duniya.

Ta ce, “Mun himmatu wajen bayar da labarun gida ga masu sauraron duniya,” in ji ta.

Yayin wani taron manema labarai a Abuja za a sanar da cikakkun bayanai kan shirin fitar da fim din da kwanan wata.

mandate
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
mandate
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Sabbin Naɗe-Naɗe 10 Da Shugaba Tinubu Ya Yi Jiya

Sabbin Naɗe-Naɗe 10 Da Shugaba Tinubu Ya Yi Jiya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.