• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamar Buhari Da Ganduje: Darius Ishaku Ya Nemi Gafarar ‘Yan Taraba

by Sadiq
2 years ago
Taraba

Gwamna Darius Dickson Ishaku na Jihar Taraba, ya nemi afuwar mutanen Taraba wadanda gwamnatinsa ta yi wa ba daidai ba na shekaru takwas.

Ishaku ya nemi gafarar ne a yayin taron godiya da kungiyar kiristoci ta kasa reshen Jihar Taraba ta shirya a sakatariyar CAN da ke Jalingo.

  • Yau Tinubu Zai Dawo Nijeriya Bayan Ya Shafe Kwanaki 34 Baya Kasa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 63, Sun Ceto Mutum 150 Da Aka Sace

Gwamnan ya ce ya yi farin ciki da yadda littafinsa na “Ba Ni Zaman Lafiya Zan Baku Ci Gaba” ya samu gindin zama a zukatan ’yan Taraba, inda ya bukaci jama’a da su bar ruhin zaman lafiya da soyayya da gafara ya jagoranci halayensu da ayyukansu.

Ishaku dai ya yi godiyar Easter a Cocin Anglican Mayo Dasa da ke Jalingo, babban birnin jihar babban birnin Jihar.

“A matsayina na shugaban da ya jagoranci jihar nan kusan shekaru takwas, mai yiwuwa na yi wa mutane da yawa laifi ko dai da sanina ko kuma cikin rashin sani a dalilin gudanar da ayyuka a matsayina na Gwamna,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Ishaku ya bayyana cewa Littafi Mai Tsarki ya ce ya fito fili ya nemi gafarar wadanda watakila ya yi wa laifi.

“A cikin Littafi Mai Tsarki, an koya mana mu gafarta wa wadanda suka yi mana laifi. A wannan yanayin, ina rokon wadanda na yi wa laifi su gafarta min. Na yi haka ne a dakin Allah, idan kuma ba su yafe min ba, tsakanin su da Allah ne,” in ji shi.

Gwamnan mai barin gado ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi hikimar yi wa al’ummar jihar hidima yadda ya kamata duk da kalubalen da gwamnatinsa ta fuskanta.

Sai dai ya bukaci al’ummar jihar da su bai wa magajinsa Laftanar Kanar Kefas Agbu (mai ritaya) goyon baya da hadin kai domin samun nasara.

Wannan dai shi ne karo na biyu da gwamnan zai je gaban taron jama’a domin neman gafarar ‘yan siyasa da al’ummar Taraba a bainar jama’a kan batutuwa da wuraren da ya bata musu rai.

A makon da ya gabata, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kuma roki ‘yan Nijeriya da ya yi wa laifi su yafe masa.

Mako guda kafin Buhari ya nemi yafiar jama’a, Gwamna Abdullahi Ganduje na Jihar Kano, ya nemi jama’a su gafarta masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Next Post
Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.