• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamar Buhari Da Ganduje: Darius Ishaku Ya Nemi Gafarar ‘Yan Taraba

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Kamar Buhari Da Ganduje: Darius Ishaku Ya Nemi Gafarar ‘Yan Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Darius Dickson Ishaku na Jihar Taraba, ya nemi afuwar mutanen Taraba wadanda gwamnatinsa ta yi wa ba daidai ba na shekaru takwas.

Ishaku ya nemi gafarar ne a yayin taron godiya da kungiyar kiristoci ta kasa reshen Jihar Taraba ta shirya a sakatariyar CAN da ke Jalingo.

  • Yau Tinubu Zai Dawo Nijeriya Bayan Ya Shafe Kwanaki 34 Baya Kasa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 63, Sun Ceto Mutum 150 Da Aka Sace

Gwamnan ya ce ya yi farin ciki da yadda littafinsa na “Ba Ni Zaman Lafiya Zan Baku Ci Gaba” ya samu gindin zama a zukatan ’yan Taraba, inda ya bukaci jama’a da su bar ruhin zaman lafiya da soyayya da gafara ya jagoranci halayensu da ayyukansu.

Ishaku dai ya yi godiyar Easter a Cocin Anglican Mayo Dasa da ke Jalingo, babban birnin jihar babban birnin Jihar.

“A matsayina na shugaban da ya jagoranci jihar nan kusan shekaru takwas, mai yiwuwa na yi wa mutane da yawa laifi ko dai da sanina ko kuma cikin rashin sani a dalilin gudanar da ayyuka a matsayina na Gwamna,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Ishaku ya bayyana cewa Littafi Mai Tsarki ya ce ya fito fili ya nemi gafarar wadanda watakila ya yi wa laifi.

“A cikin Littafi Mai Tsarki, an koya mana mu gafarta wa wadanda suka yi mana laifi. A wannan yanayin, ina rokon wadanda na yi wa laifi su gafarta min. Na yi haka ne a dakin Allah, idan kuma ba su yafe min ba, tsakanin su da Allah ne,” in ji shi.

Gwamnan mai barin gado ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi hikimar yi wa al’ummar jihar hidima yadda ya kamata duk da kalubalen da gwamnatinsa ta fuskanta.

Sai dai ya bukaci al’ummar jihar da su bai wa magajinsa Laftanar Kanar Kefas Agbu (mai ritaya) goyon baya da hadin kai domin samun nasara.

Wannan dai shi ne karo na biyu da gwamnan zai je gaban taron jama’a domin neman gafarar ‘yan siyasa da al’ummar Taraba a bainar jama’a kan batutuwa da wuraren da ya bata musu rai.

A makon da ya gabata, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kuma roki ‘yan Nijeriya da ya yi wa laifi su yafe masa.

Mako guda kafin Buhari ya nemi yafiar jama’a, Gwamna Abdullahi Ganduje na Jihar Kano, ya nemi jama’a su gafarta masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDarius IshakuGandujeNeman GafaraTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yau Tinubu Zai Dawo Nijeriya Bayan Ya Shafe Kwanaki 34 Baya Kasa

Next Post

Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

Related

gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

24 minutes ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

2 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

3 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

4 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

5 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

7 hours ago
Next Post
Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

LABARAI MASU NASABA

gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.