• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamar Buhari Da Ganduje: Darius Ishaku Ya Nemi Gafarar ‘Yan Taraba

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Kamar Buhari Da Ganduje: Darius Ishaku Ya Nemi Gafarar ‘Yan Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Darius Dickson Ishaku na Jihar Taraba, ya nemi afuwar mutanen Taraba wadanda gwamnatinsa ta yi wa ba daidai ba na shekaru takwas.

Ishaku ya nemi gafarar ne a yayin taron godiya da kungiyar kiristoci ta kasa reshen Jihar Taraba ta shirya a sakatariyar CAN da ke Jalingo.

  • Yau Tinubu Zai Dawo Nijeriya Bayan Ya Shafe Kwanaki 34 Baya Kasa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 63, Sun Ceto Mutum 150 Da Aka Sace

Gwamnan ya ce ya yi farin ciki da yadda littafinsa na “Ba Ni Zaman Lafiya Zan Baku Ci Gaba” ya samu gindin zama a zukatan ’yan Taraba, inda ya bukaci jama’a da su bar ruhin zaman lafiya da soyayya da gafara ya jagoranci halayensu da ayyukansu.

Ishaku dai ya yi godiyar Easter a Cocin Anglican Mayo Dasa da ke Jalingo, babban birnin jihar babban birnin Jihar.

“A matsayina na shugaban da ya jagoranci jihar nan kusan shekaru takwas, mai yiwuwa na yi wa mutane da yawa laifi ko dai da sanina ko kuma cikin rashin sani a dalilin gudanar da ayyuka a matsayina na Gwamna,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Ishaku ya bayyana cewa Littafi Mai Tsarki ya ce ya fito fili ya nemi gafarar wadanda watakila ya yi wa laifi.

“A cikin Littafi Mai Tsarki, an koya mana mu gafarta wa wadanda suka yi mana laifi. A wannan yanayin, ina rokon wadanda na yi wa laifi su gafarta min. Na yi haka ne a dakin Allah, idan kuma ba su yafe min ba, tsakanin su da Allah ne,” in ji shi.

Gwamnan mai barin gado ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi hikimar yi wa al’ummar jihar hidima yadda ya kamata duk da kalubalen da gwamnatinsa ta fuskanta.

Sai dai ya bukaci al’ummar jihar da su bai wa magajinsa Laftanar Kanar Kefas Agbu (mai ritaya) goyon baya da hadin kai domin samun nasara.

Wannan dai shi ne karo na biyu da gwamnan zai je gaban taron jama’a domin neman gafarar ‘yan siyasa da al’ummar Taraba a bainar jama’a kan batutuwa da wuraren da ya bata musu rai.

A makon da ya gabata, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kuma roki ‘yan Nijeriya da ya yi wa laifi su yafe masa.

Mako guda kafin Buhari ya nemi yafiar jama’a, Gwamna Abdullahi Ganduje na Jihar Kano, ya nemi jama’a su gafarta masa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariDarius IshakuGandujeNeman GafaraTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yau Tinubu Zai Dawo Nijeriya Bayan Ya Shafe Kwanaki 34 Baya Kasa

Next Post

Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

9 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

10 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

11 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

13 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

18 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

19 hours ago
Next Post
Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

Tinubu Da Matarsa ​​Sun Dawo Abuja Daga Faransa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.