• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamata Ya Yi A Yi Hadin Gwiwa Da Sin Don Cin Gajiyar Kimiyya Da Fasaha Ba Wai Adawa Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kamata Ya Yi A Yi Hadin Gwiwa Da Sin Don Cin Gajiyar Kimiyya Da Fasaha Ba Wai Adawa Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan lokaci da duniya ke fuskantar yanayi na saurin fadadar ci gaban fannonin kimiyya da fasaha, da takara mai tsanani tsakanin sassa daban daban, ko shakka babu kasar Sin ta ciri tuta, wajen zama ginshiki mai karfi a bangaren cin gajiyar fannonin kimiyya da fasaha daban daban, wanda a ganin masharhanta da dama, hakan ya samar da dama ga daukacin duniya na cin gajiya tare. 

 

To sai dai kuma, a hannu guda matakin Amurka na baya bayan nan, na hana Amurkawa zuba jari a wasu sassan kimiyya da fasaha na kasar Sin, ya haifar da tarnaki ga cin gajiya tare tsakanin kasashen biyu, kana hakan ya nuna rashin fahimtar Amurka game da ainihin halin da duniya ke ciki ta wannan fanni.

  • An Yanke Wa Mai Haƙar Ma’adanai Hukuncin Shekara 1 Saboda Satar Waya
  • Gwamna Sani Ya Amince Da ₦72,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Jihar Kaduna 

Sanin kowa ne cewa, Sin ta riga ta cimma wani mataki mai nisa na ci gaban kimiyya da fasaha, wadanda ake iya gani a zahiri idan an bibiyi mujallun yada ilimi, da makaloli, da sakamakon ayyukan bincike daban daban. Hakan ne ma ya sa hukumar lura da kare ikon mullakar fasaha ta kasa da kasa ko WIPO, ta ce Sin din ce kan gaba a duniya wajen yawan masu gabatar da bukatun rajistar mallakar fasaha. Alal misali, a shekarar 2019, Sin ta tsallake Amurka wajen zama kasa ta daya a duniya, da alummar ta suka gabatar da mafi yawan irin wadannan bukatu na rajista.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

Don haka matakin Amurka na kakaba takunkumin zuba jari a kasar Sin, a fannonin samar da sassan hada latironi ko semiconductors, da fannin kirkirarriyar basira ko AI, da fasahar manyan lissafi da na’urori masu kwakwalwa ko quantum technology, zai illata ita kanta Amurkan.

 

Don haka a gani na, maimakon Amurka ta dauki irin wadannan matakai na “A fasa kowa ya rasa”, ko fito na fito, kamata ya yi ta rungumi dukkanin wasu hanyoyi na raya hadin gwiwa, ta yi tarayya da Sin a matsayin abokiyar gudanarwa, da cin gajiyar sakamakon da Sin ke samu a fannin raya ilimin kimiyya da fasaha.

 

Sassan biyu suna iya cimma hakan ne kawai, idan sun rungumi juna, sun yi aiki tare a fannonin bincike, musayar fasaha, da raba kwarewa, musamman a bangarorin nazarin sauyin yanayi, kiwon lafiya, da sauran bukatun bil adama na bai daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Magoyin Bayan Manchester United Ya Rasa Ransa A Dalilin Musun Kwallo A Uganda 

Next Post

Jihohin Da Suka Amince Su Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata

Related

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

10 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

11 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

13 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

15 hours ago
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

17 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

17 hours ago
Next Post
Jihohin Da Suka Amince Su Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata

Jihohin Da Suka Amince Su Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Ma'aikata

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.