• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfani Ya Yaye Masu Kirkirar Fasaha 1,000 A 2023

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Kamfani Ya Yaye Masu Kirkirar Fasaha 1,000 A 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin ALX Nigeria ta yaye masu kirkirar fasaha sama da 1,000 a cikin shirinta na shekarar 2023 tare da shan alwashin jan damara wajen cigaba da nemo mafita ga matsalar da Nijeriya ke fuskanta na marasa aikin yi.

Da ta ke jawabi a wajen bikin yayen wanda ya gudana a Legas, Ruby Igwe, manajan ALX a Nijeriya, ta bada tabbacin yunkurinsu na bai wa ‘yan kasuwa masu tasowa dabaru da hikimomi kan amfani da fasaha da hakan zai taimaka sosai wajen bunkasa cigaban tattalin arzikin kasar nan da kuma habakarta.
Ruby Igwe, ta kuma jinjina ma wadanda aka yayen bisa jajircewarsu wajen koyon abubuwan da ake son su koya a karkashin shirin.

  • Kasafin 2024: Tinubu Ya Umarci Ma’aikatu Su Rika Ba Da Rahoton Ayyukansu Duk Wata
  • Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen

“ALX ta maida hankali wajen koyarwa da bada tallafin karatu. Kun kasance a nan ne saboda jajircewarku da himmarku.
“Afrika na fama da matsalar matasan da ba su yi karatu ba da marasa aikin yi. ALX Nigeria da Africa sun dukufa wajen ganin sun tallafa wa matasa miliyan uku da kwarewa a bangaren fasaha da zai yi hayar taimakonsu a ayyukansu na gaba da kasuwancinsu,” ta shaida.

Fasaha

Ta taya wadanda aka yayen murna da basu tabbacin samun goyon baya da tallafi a kowani lokaci, “kungiyar nan za ta cigaba da kasancewa a nan domin ku, kuma za mu tunkari matsalolin da za ku fuskanta a tare hanaki daya. Sannan, za mu kasance masu baku shawarori daga kwararrun masana da dauraku a hanyoyin da suka dace domin rayuwa ta ke inganta.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

Aledandra Edem, daya daga cikin wadanda aka yaye ta bayyana yadda ta samu horon, “wannan horon shi ne irinsa na farko da na fara na kammala ba tare da ciwon kai da shan wahala ba. A lokacin da ka shiga koyon a wasu wuraren, za ka ji koyon bai dace da kai ba. Amma a nan mutum zai gamsu har ma ya samu cikakken horon da ake son ya koya da shirin samun damar makin ayyuka.”

Fasaha

Wata karin wacce aka yaye, Temitope Nelson, ta ce, “baya ga kwarewar da muka samu a bangaren fasaha, gidauniyar ta kasance cibiyar koyar da yadda mutum zai samu gogewa wajen hada manhajoji. Na koyi yadda zan tafiyar da abubuwan da kaina da wasu, zan iya kasancewa mai dogaro da kaina na kuma taimaki wasu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban MatasaKasuwanciTabarbarewar tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Fitar Da Shirin Bunkasa Cin Gajiya Daga Bayanai Ko Data

Next Post

Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

Related

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

21 hours ago
Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
Tattalin Arziki

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

2 days ago
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

2 days ago
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

1 week ago
Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

2 weeks ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

3 weeks ago
Next Post
Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.