• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
10 months ago
in Dausayin Musulunci
0
SAW
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yana daga cikin abunda zai nuna maka kamshin Annabi da duk abin da ya fita a jikinsa, shan jinin Annabi da Imam Malik bin Sinanin, Abi Kudri ya yi a ranar yakin Uhudu. Sannan kuma Annabi ya yi mai bushara da cewa wuta ba za ta ci shi ba.

 

Irin wannan Hadisi ya faru da Zubairu bin Awwam, mijin Asma’u ‘yar Sayyidina Abubakar uwar Abdullahi bin Zubair dan da aka fara haifa a Madina bayan Hijra.

  • Mawakiyar Yabon Fiyayyen Halitta Annabi (SAW), Rukayat Gawat Ta Rasu
  • Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

Wata rana Zubairu bin Awam ya yi wa Annabi Muhammad (SAW) kaho, sai Annabi ya yi masa umarni da ya je ya zubar da jinin, bayan ya je zubarwa sai ya shanye jinin, da ya dawo sai Annabi ya fahimci hakan a fuskarshi, sai ya ce masa ka sha jinina? sai Annabi ya ce masa “Wailul laka minannasi, wa wailul lahum minka – kaicon ka da mutane kuma su ma kaicon su da kai”. Annanbi (SAW) bai yi inkarin shan jininsa ba.

An sake ruwaito irin wannan hadisi a cikin (sha’anin) wata mata, wacce ta sha fitsarinsa (SAW), ita ce Barakatu ko Ummu Aimana, Annabi (SAW) ya ce mata kika sha Fitsari na! ba za ki kara ciwon ciki ba.

Labarai Masu Nasaba

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)

Amma Annabi (SAW) bai taba umartar daya daga cikin wadanda suka sha jininsa ko fitsarin sa da wankewa ko kuskure baki ba sannan kuma bai taba ce musu kar su kara ba. Hadisin wadanda suka sha jinin Annabi ingantacce ne duk a wurin Malamai.

Hadisin wannan mata mai shan fitsarin Annabi an yi sabani a cikin wacce ta sha fitsarin, wasu sun tafi cewa Ummu Aimana ce wacce ta raini Annabi wasu kuma sun tafi a kan ‘yar dakin ‘yar Abu Sufyan ce Matar Annabi, kadimar Annabi (SAW). Yadda abin yake shi ne akwai wani sassaken Dabino da aka yi shi kamar akushi ana shigar da shi inda Annabi yake da dare don yin fitsari a cikinsa, ana ajiye shi a karkashin gado, wata rana sai wannan mata ta tashi tana jin kishin ruwa, garin lalube sai ta ga wannan abu da ruwa mai aminci a cikinshi, sai tasha, da safe Annabi ya ce a fitar da fitsari, sai wannan mata ta ce “ya Rasulullahi na tashi cikin dare ni kuma ina jin kishin ruwa, ina neman ruwa sai na ga wannan ni kuma sai na shanye, ni kuma ban san meye ba.” Ibn Juraidu da sauran Malamai duk sun ruwaito wannan Hadisi.

Manzon Allah (SAW), an haife shi da Kaciyarshi kuma abun yanke wa Cibiya, in ji Shaffa’u.

An karbo daga Mahaifiyarsa, Aminatu (RA) ta ce na haife shi tsarkakakke ba shi da wata kazanta. Kuma an karba daga Sayyada A’isha Ummul Muminina tana cewa ban taba ganin tsiraicin Annabi (SAW) ba.

An karba daga Sayyidina Ali Karramalahu wajhahu yana cewa Annabi Muhammad (SAW) ya yi mun wasiyya yana mai cewa “Kar in bar wani ya yi mai wanka sai ni” sabida Annabi ya ce min “babu wanda zai ga Al’aurata face an shafe idanuwansa”, ma’ana karshen rayuwa zai makance kamar yadda duk wadanda suka ga Mala’ika Jibrilu su ma akarshen rayuwa sun makance.

An karbo daga Hadisin Ikrama cewa wata rana Annabi ya yi bacci, har ana jin minsharinsa, da aka kira Sallah sai ya tashi ya yi Sallah bai yi Alwala ba, sai Ikrima ya ce “Shi Annabi Muhammad (SAW) ya kasanace abin kiyayewa ne ko bacci yake ya san abin da ke faruwa”.

Yanzu kuma a wannan zango za mu yi magana a kan cikar Hankalinsa da Fasahar harshensa (SAW).

Cikar hankalin Annabi: Idan muka yi duba zuwa ga cikar hankalinsa da kaifin fahimtarsa da karfin masu riskarsa (Abu biyar) da fasahar harshensa da daidaiton motsinsa (ba bazo-bazo ko kasalanci) da kyawawan dabi’unsa babu kokonto, Annabi ya kasance mafi hankalin mutane kuma mafi kaifin fahimtarsu, musamman idan aka yi la’akari da yadda Annabi yake shirya abubuwan boye na halitta – abun da zuciyarsu ta shiryu da shi, da yadda ya shirya musu lamarin bayyanensu – Lamarin yadda suke gudanar da rayuwa ta yau da kullum da yadda ya shirya abubuwan da za su amfani sauran halitta da yadda ya shirya wa kebantattu tsarin rayuwarsu tare da ban mamakin dabi’unsa da kayatarwa a tarihinsa, balle kuma mutum ya duba abubuwan da ya kwaranyo na Ilimi sannan ya tabbatar na daga Shari’a ba tare da ya koya daga kowa ba ko a ce an yi gogayya ko ya karanta a littattafan da suka gabata, duk ba a yi wannan ba, daga Allah yake.

Malam Wahabu, masanin ilimin Yahudu da Nasara sannan ya kara da na Musulunci ya fada yana cewa “Na karanta littattafai Saba’in da daya na Yahudu da Nasara sai na samu a cikin dukkan wannan littattafai, cewa lallai Annabi Muhammadu (SAW) shi ne mafi rinjayen mutane a hankali kuma shine mafificinsu wajen ra’ayi.

A cikin wata ruwaya ta wannan malami, ya ce “Sai na samu a cikin dukkan wadannan littattafai da aka saukar wa Annabawa cewa lallai Allah bai ba wa mutane tun daga farkon duniya har izuwa karshenta na daga hankali ba idan aka gwada da na Annabi Muhammad (SAW), face sai ka samu (tamkar) kwayar rairayi ce a cikin fadin duk yawan saharar duniya.”

Yana nufin, hankallin mutanen duniya daga farko izuwa karshe shi ne kwayar rairayin, na Annabi kuwa shi ne yawan fadin duk saharar Duniya.

Malam Mujahidu ya ce, Manzon Allah (SAW) ya kasance, idan ya tashi zai ja Sallah, yana ganin duk wadanda ke bayan shi kamar yadda yake ganin duk wanda yake gabanshi, da wannan magana ce malamai suka fassara ayar “Watakallubaka fis sajidin – da jujjuyawarka a cikin masu Sujada”

Ya zo a cikin Littafin Muwadda ta Imam Malik, daga Annabi (SAW) yana cewa “Ni ina ganinku ta bayana” an kuma karba irin wannan Hadisin daga Anas a cikin Bukhari da Muslim.

An karba daga Sayyada A’isha (RA) irin wannan Hadisin tana cewa “Meye abun mamaki don an ce Annabi yana gani ta baya, ai kari ne cikin Mu’ujizozinshi”

Annabi Muhammad (SAW) an dauko masa Sarkin Habasha, Najashi lokacin da ya rasu yana Habasha, Annabi Yana Madina amma yace da Sahabbai ku tashi mu yi Sallah, Najashi ya rasu. Sahabbai suka ce ba ma shakkar Najashi yana nan kwance a gaban Annabi. An kuma dauko masa Baitul Makdisi yayin da Kuraishawa suka nemi ya siffanta musu Masallacin kan batun Isra’i kuma an sake dauko masa Ka’aba lokacin da ya gina Masallacinsa a Madina, yayin kafa alkiblar masallacin, sannan malamai sun yi Hikaya cewa Annabi yana ganin duk Taurarin cikin Surayya guda 12. Duk wadannan abubuwan da muka lissafa na daga Sallar Najashi, Siffanta Baitul makdisi, aza alkiblar Masallacinsa zuwa Ka’aba, Ganin taurarin Surayya duk da idanunsa na ka guda biyu ya gansu, in ji Ahmadu bin Hambali da waninsa.

Abi Huraira ya karbo Hadisi daga Annabi (SAW), ya ce yayin da Allah ya yi Tajalli (Bayyana) ga Annabi Musa (AS), tun daga nan Annabi Musa (AS) ya fara ganin kiyashi a kan babban dutse mai nisan tafiyan mil 30 a cikin dare mai duhu. In dai Annabi Musa (AS) Sabida ganin Tajallin Allah ya fara ganin irin wannan, to ina Annabi Muhammad (SAW) da ya ga “Min  Ayati Rabbihil Kubra”, ta yaya zai zama abin kuskure kan cewa Annabi yana gani ta bayansa kamar yadda yake gani ta gabansa.

Hakika labarai sun zo cewa Annabi Muhammad (SAW) ya kada Rukanata, wanda Rukanata shi ne mafi karfin ‘yan zamaninsa. Yadda abin yake shi ne, wata rana Annabi Muhammad ya kira Rukanata da ya shiga Musulunci, sai Rukanata ya ce shi dan kokawa ne don haka sai an yi kokawa an kayar da shi zai amshi musulunci, sai Annabi ya amince da sharadin Rukanata, sai da aka kayar da Rukanata sau Uku, duk juyi yana cewa bai shirya ba amma a karshe ya amshi Musulunci.

Abi Hurairata yana cewa “Ban taba ganin wanda ya fi Annabi sauri da gaggawa ba cikin tafiyarsa, sai mun hada da sassarfa kana muke cimmasa”.

Yana daga cikin siffofin Annabi Muhammad (SAW) cewa dariyarsa, Murmushi ce sannan idan zai juya gaba daya yake juyawa, ba ya waige kuma in yana tafiya kamar ciccira yake yi kamar yana gangarowa daga tudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahangar Masana Kan Yawaitar Ibtila’i A Arewa

Next Post

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Related

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

6 days ago
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (3)

2 weeks ago
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

3 weeks ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

1 month ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

1 month ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

2 months ago
Next Post
abinci

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.