ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahangar Masana Kan Yawaitar Ibtila’i A Arewa

by Shehu Yahaya
2 years ago
Arewa

Kafin shekara ta 2007, yankin Arewacin Nijeriya ke sahun gaba wajen samun dauwamammen zaman lafiya da wadatar abinci saboda arzikin noma da kiwo wanda yake iya kaiwa ko ina a fadin Nijeriya da kasashen da ke makwabtaka da ita, baya ga hada-hadar harkokin kasuwanci.

Sai dai daga bisani, yankin ya fara shiga cikin ibtila’in rashin tsaro da koma-bayan tattalin arziki sannan ga ibtila’in ambaliyar ruwa wanda ko a bana sai da abin ya faru a jihohi irin su Jigawa da Kaduna da Kebbi da Kano, da kuma na baya-baya nan na Jihar Borno, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da asarar dukiya. Bugu da kari, akwai kuma ibtila’in kifewar kwalekwale daban-daban da suka faru a jihohin Kebbi da Zamfara wanda ta lakume rayuka masu dimbin yawa.

  • Jarin Kai Tsaye Na Waje Da Ba Na Kudi Ba Da Sin Ta Zuba A Ketare Cikin Watanni 8 Na Farkon Bana Ya Kai Dala Biliyan 94.09
  • Karin Harajin Amurka Ba Zai Dakile Sashen Kere-Keren Kasar Sin Ba

Masana sun bayyana samun yawaitar ibtila’i a jihohin Arewa a matsayin alamun karshen duniya, yayin da wasu suka ce akwai sakacin shugabannin yankin, wasu kuma suka alakanta lamarin da rashin bin dokokin Allah.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP Hausa ta tattaro ra’ayin malaman addinin Musulunci da na Kirista da masanin falsafa domin jin mene ne musabbabin wadannan ibtila’o’i musamman ganin cewa a arewa ne abubuwan suka fi kamari, kana da kuma hanyoyin samun mafita kan irin wadannan musibu da suka addabi arewar.

Shugaban sashin falsafa na tsangayar fasaha ta jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Dakta Abubakar Zariya Ibrahim ya ce a bangaran falsafa, “Muna hangen lamarin a matsayin kaddara da kuma yardar Allah.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Arewa

Kaddara shi ne wani abu da Allah ya aiko da shi, to amma ya yarda da abin? Alal misali, idan barawo ya yarda ga Allah ne ya kaddara a yi satan, toh Allah ya yarda a yi? Saboda haka sata kaddara ce, amma Allah bai yarda a yi ta ba.

“A falsafance, yawacin musibun nan a irin wannan suke fadowa, wato kaddara da yardar Allah, saboda Allah ne ya kaddara da su amma bai yarda ba, kamar yadda ya kaddara sata amma bai yarda a yi ta ba.
“Yawancin irin wadannan musibu a irin wannan ma’aunin suke, a takkaice kenan. Yanzu bari mu fara da ibtila’in madatsar Alo da ke Jihar Borno, to ka ga wannan ba bangaren da Allah ya yarda da shi ba ne.

“Idan muka duba A 2015, akwai wani binciken masana irin su Dakta Babagana da Bungus da Kolo da Bello suka yi sun nuna irin hadarin da madatsar ruwan take da shi kuma suka nuna bukatar gaggawa ta kula da take nema na gyara, amma gwamnati ba ta dauki mataki ba.

“A 2022, masana irinsu Dakta Lala da Jibril da Umar da Sadik sun yi bincike kan yadda ake gudanar da mulki da ita kanta madatsar ruwan ta Alo dangane da irin hadarin da take ciki da kuma bukatar gyaran gaggawa, amma dukka gwamnati ba ta yi komai a kai ba.

“Kar ka manta duk da afkuwar wannan abu da za mu kira shi kaddara, gwamnati Borno ta aika da tawaga ta musamman wurin domin su je su gano halin yadda wurin yake ciki. Sai suka fada wa duniya cewa babu wata matsala. Kuma babu abin da zai faru. Ba a yi sati biyu ba, sai ambaliyar ta faru.

“Tun daga shekarar 2020 zuwa 2024, gwamnatin ta fitar da kudi domin a gyara wannan dam din. A irin wannan lokacin ne ma’aikatar albarkatun ruwa ta Jihar Borno ta ce ta kashe kudi naira biliyan 6.5 wajen aikin ofis, amma ita madatsar ruwan babu komai.

“Abin tambaya a nan, barkewar madatsar ruwar kaddara ce ko ganganci? Saboda mu ba za mu kirashi kaddara ba. Sai dai ganganci saboda wannan ba ibtila’i ne daga Allah ba, wanda za a ce ba a san da zuwansa ba.

“Idan muka dauki barayin daji, wannan makarkashiya ce tun shigowar mulkin soja, wato lokacin Ironsy har zamanin Abdulsalam aka dasa mana wannan matsala.

“A lokacin su Sardauna sun rinka shiga lungu da sako suna gina makarantu da hanyoyi, wanda lokacin Turawa an gina titin jirgin kasa ne kadai. Zaman lafiya shi yake haifar da yaduwar ci gaba. Akwai sakacin gwamnati wajen samun ibtila’i. A lokacin zamanin mulkin Yakubu Gowon, gwamnati ta samu kudi ba karami ba a Nijeriya. A lokacin gwamnati ta ce ba ta san mai za ta yi da kudi ba, baya ga lokacin akwai kauyuka da manyan rugage wadanda ba su da ofishin ‘yansanda, ba su da makaranta da asibitoci ballantana titi da zai kawo su cikin gari, da lokacin an yi musu wadannan abubuwa da yanzu duk irin wannan matsalar ta ‘yan fashin daji da babu su.

“Ka ga rashin ilimi da abinci babu ofishin ‘yansanda da za su nuna musu yadda doka take idan da akwai su da ba a sama wannan matsalar ba.”

“Haka kuma akwai bukatar sai gwamnati ta inganta rayuwar al’umma ta bangarori daban-daban idan aka yi haka za a dan samu sauki.” Kamar yadda ya bayyana.

Shi kuwa a mahangarsa, Malamin addini Musulunci, Sheikh Halliru Maraya da ke Jihar Kaduna, ya bayyana cewa rashin tsoron Allah ne ya haifar da irin jarabobin da suke addabar arewacin kasar nan duba da yadda al’ummar yankin suka yi watsi da dokokin Allah.

Arewa

Malam Maraya ya ce a yanzu aikata miyagun laifiku karuwa suke, wanda muddin aka ci gaba da haka, to babu shakka an kulla abota da shiga musibu kala-kala.

Ya ce, “Ina mai tabbatar maka da cewa sabon Allah ke jawo musiba, wanda yake shafar wanda ya sani da wanda bai sani ba. Wani lokaci kuma sai ka tarar da mutane suna aikata laifi amma Allah sai ya saukar musu da ni’ima. Shi Allah yakan musu haka ne kafin ya kama su.

“Idan za a ci gaba da sabon Allah, to za a ci gaba da samun musiba iri daban-daban a arewacin kasar nan. Allah ya ce ku ji tsoron musiba saboda idan ta zo za ta shafi azzalumai da mutanan kirki. Saboda haka yawaitar sabon Allah shi ne dalilin shiga ibtila’in da ake samu a kasar nan baki daya.”
Shehin Malamin ya kuma bayyana cewa mafita ita ce a koma ga Allah wajen bin dokokinsa, wanda ta haka ne a za a masu saukin irin wadannan musibun.

“A mahanga ta addinin Musulunci mafita ita ce, tsoron Allah. Allah ya ce duk wanda ya ji tsoro Allah, to zai kawo masa mafita. Wadannan musibu na Arewa mafita shi ne, a ji tsoron Allah a rika aikata abin da Allah ya ce, idan aka yi haka, to kamar yadda ya yi alkawari za a samu mafita.

A nasa bangaren, Shugaban Cocin ‘Christ Ebangelical and Life Intervention Ministry’ da ke Barnawa a Jihar Kaduna, Fasto Yohanna Buru ya ce irin wadanan ibtila’in da ke fuskantar yankin Arewacin Nijeriya alamu ne na karshen duniya, musamman ganin yadda malaman addinai suka zama ‘yan amshin shata, su kuma shugabanin babu tausayi da rashin rikon amanar mabiyansu.

Arewa

Fasto Buru wanda yana daga cikin fastoci da yake rajin samar da zaman lafiya da hadin kan ‘yan Arewa, ya ce rashin adalci shi ne ya haifar da rashin tsaro. Ya ce akwai rashin tsoron Allah, inda aka fifita son duniya kan tsoron Allah.

“Mu a arewa babu yunwa saboda babu fari, domin fari shi ke kawo yunwa. ‘Yan Arewa su ne suka haifa wa kansu matsala da musiba. Wadannan musibu da suke samun arewa alamun tashin duniya ne, malamai da shugabanni babu tausayin talakawa a kansu.”

Faston ya ce muddin ana bukatar neman mafita, sai a yi taron yi wa kasa addu’a, wanda za a hada malaman addinai da sarakuna da dattawan arewa da sauran talakawa a yi addu’ar samun mafita.
“Shekara goma sha daya kenan ina kiran a samu hadin kan ‘yan arewa domin magance afkuwar irin wadannan musibu, amma shugabannin na Arewa sun ki su kula hakan.” In ji shi.

Matsalar yawaitar afkuwar ibtila’o’i a arewa musamman a ‘yan shekarun nan dai aba ce da ta addabi galibin al’ummar yankin, don haka ya sa aka yi kokarin shirya tarurruka ciki har da wanda aka gabatar game da sha’anin tsaro a Abuja a kwanan baya. Sai dai rashin aiwatar da kudirorin da aka cimma a aikace na kara dagula lissafin lalubo bakin zaren magance lamarin.

Arewa
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
SAW

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.