• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kan Mage Ya Waye, Turawan Yamma A Sake Lale Kan Yamadidin “Tarkon Bashin Sin”

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kan Mage Ya Waye, Turawan Yamma A Sake Lale Kan Yamadidin “Tarkon Bashin Sin”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ya dace zuwa yanzu kowa ya fahimci kulafacin da Turawan Yamma ke nunawa a kan kawancen da kasar Sin ke yi da kasashen duniya musamman masu tasowa wajen samar da damammaki domin cin gajiyar juna. 

Shaci-fadi da farfagandar wofi sun mamaye rahotannin da kafafen yada labarun yamma ke bayarwa a duk wani abu da ya shafi kawancen ci gaba na Sin da kawayenta.

  • Wane Irin Hadari Amurka Take Son Ta Kawar?

Ko da Turawan suka ga sun kasa tarwatsa kawancen, sai suka bullo ta bayan gida ta hanyar yamadidin cewa kasar Sin na dankara wa kasashe masu tasowa basussuka na rashin imani inda suka yi wa abin lakabi da “Tarkon Bashin Sin”.

Amma domin rabe zare da abawa, wani bincike da aka gudanar kwanan nan a wasu kasashe kamar Pakistan, Kenya, Zambia da Sri Lanka, ya yi tonon silili ga yamadidin kambama basussukan da Sin ke bai wa kasashen domin ayyukan bunkasa ababen more rayuwa da raya kasa.

Kididdiga ta nuna cewa, daga cikin bashin da Kenya ta ci a kasashen waje kimanin Dala biliyan 36.66 zuwa watan Maris din 2023, kashi 17.2 cikin dari ne na Sin, a yayin da hukumomin kudi na tsakanin bangarori da dama ke bin ta kaso 46.3%, ciki har da asusun ba da lamuni na duniya (IMF) da bankin duniya da sauransu. Ita kuwa Pakistan zuwa watan Afrilun 2023, tana da bashin waje a kanta Dala biliyan 125.702, daga ciki du-du-du na Sin bai wuce Dala biliyan 20.375 ba, kimanin kashi 16.2 cikin dari.

Labarai Masu Nasaba

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

A Zambia, basussukan waje da kasar ta ci zuwa karshen 2022 sun kai na Dala biliyan 18.6, daga ciki Dala biliyan 6 ne na Sin. Haka nan idan aka dubi Sri Lanka, basussukanta na waje zuwa watan Maris, 2023 sun kai Dala biliyan 27.6, daga wannan adadin kwata-kwata na Sin bai wuce Dala biliyan 3 ba, kimanin kashi 10.8 a cikin dari.

Don haka ta ina ne basussukan Sin suka zama karfen kafa ga kasashen da take kawance da su? Ko dai abin nan ne da Hausawa ke cewa, “idan an tsani mutum ko ruwa ya shiga sai a ce ya tayar da kura.”

An ce “gwano ba ya jin warin jikinsa”, su kasashen yamma sun fi kowa dankara wa kasashe bashi da mugun kudin ruwa. Ba zan manta ba, shi ya sa a zamanin mulkin tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo (1999-2007) ya niki gari har kasashen Turawan na yamma ya shaida musu cewa Nijeriya ba za ta iya biyan basussukan da suke bi ba, saboda dankaren kudin ruwa, sai dai su yafe kawai!

Kamar yadda Obasanjo ya koka da dankaren kudin ruwan basussukan yamma, shi ma shugaban wata cibiyar binicke kan bunkasa tattalin arziki da ci gaba a zamanance ta Asiya da ke Pakistan, Shakeel Ahmad Ramay ya ce, “Babbar matsalarmu ita ce basussukan da muka ci daga hukumomin kudi na kasashen yamma, Pakistan ba za ta iya biyan su ba saboda basussuka ne masu dankaren kudin ruwa.”

Bayanai daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa kashi uku bisa hudun basussukan da Afirka ke ka-ka-ni-ka-yi da su daga cibiyoyin kudi ne na kasashen duniya amma ba kasar Sin ba.

Shi ya sa mataimakin sakataren kungiyar kawancen Sin da Zambia, Chibeza Mfun ya ce, “idan ma akwai abin da ya fi ci mana tuwo a kwarya a matsayinmu na kasa, shi ne biyu bisa ukun basussukan da ake bin mu. Ba kasar Sin ke bin mu biyu bisa uku ba, masu kawo gudunmawa ne daga kasashen yamma da cibiyoyin kudi.”

Maimakon yamadidi, kamata ya yi Amurka da sauran kasashen yamma su dubi yadda suke bautar da kasashe masu tasowa da kudin ruwan da suke lafta wa basussukan da suke bin su, da yayyafa wa rikicin Ukraine da suka kunna ruwa wanda yake barazana tare da nakasa kasashe masu tasowa. A halin yanzu dai kan mage ya waye, batun yamadidin “Tarkon Bashin Sin”, gidan toka ne da ake son ginawa a tsakiyar teku!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ziyarar LEADERSHIP Hausa A Hubbaren Degel Ta Mahaifin Shehu Usman Danfodiyo

Next Post

Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

Related

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

11 minutes ago
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

1 hour ago
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

2 hours ago
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

22 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

23 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

1 day ago
Next Post
Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.