ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kan Mage Ya Waye, Turawan Yamma A Sake Lale Kan Yamadidin “Tarkon Bashin Sin”

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Tarkon Bashin Sin

Ya dace zuwa yanzu kowa ya fahimci kulafacin da Turawan Yamma ke nunawa a kan kawancen da kasar Sin ke yi da kasashen duniya musamman masu tasowa wajen samar da damammaki domin cin gajiyar juna. 

Shaci-fadi da farfagandar wofi sun mamaye rahotannin da kafafen yada labarun yamma ke bayarwa a duk wani abu da ya shafi kawancen ci gaba na Sin da kawayenta.

  • Wane Irin Hadari Amurka Take Son Ta Kawar?

Ko da Turawan suka ga sun kasa tarwatsa kawancen, sai suka bullo ta bayan gida ta hanyar yamadidin cewa kasar Sin na dankara wa kasashe masu tasowa basussuka na rashin imani inda suka yi wa abin lakabi da “Tarkon Bashin Sin”.

ADVERTISEMENT

Amma domin rabe zare da abawa, wani bincike da aka gudanar kwanan nan a wasu kasashe kamar Pakistan, Kenya, Zambia da Sri Lanka, ya yi tonon silili ga yamadidin kambama basussukan da Sin ke bai wa kasashen domin ayyukan bunkasa ababen more rayuwa da raya kasa.

Kididdiga ta nuna cewa, daga cikin bashin da Kenya ta ci a kasashen waje kimanin Dala biliyan 36.66 zuwa watan Maris din 2023, kashi 17.2 cikin dari ne na Sin, a yayin da hukumomin kudi na tsakanin bangarori da dama ke bin ta kaso 46.3%, ciki har da asusun ba da lamuni na duniya (IMF) da bankin duniya da sauransu. Ita kuwa Pakistan zuwa watan Afrilun 2023, tana da bashin waje a kanta Dala biliyan 125.702, daga ciki du-du-du na Sin bai wuce Dala biliyan 20.375 ba, kimanin kashi 16.2 cikin dari.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A Zambia, basussukan waje da kasar ta ci zuwa karshen 2022 sun kai na Dala biliyan 18.6, daga ciki Dala biliyan 6 ne na Sin. Haka nan idan aka dubi Sri Lanka, basussukanta na waje zuwa watan Maris, 2023 sun kai Dala biliyan 27.6, daga wannan adadin kwata-kwata na Sin bai wuce Dala biliyan 3 ba, kimanin kashi 10.8 a cikin dari.

Don haka ta ina ne basussukan Sin suka zama karfen kafa ga kasashen da take kawance da su? Ko dai abin nan ne da Hausawa ke cewa, “idan an tsani mutum ko ruwa ya shiga sai a ce ya tayar da kura.”

An ce “gwano ba ya jin warin jikinsa”, su kasashen yamma sun fi kowa dankara wa kasashe bashi da mugun kudin ruwa. Ba zan manta ba, shi ya sa a zamanin mulkin tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo (1999-2007) ya niki gari har kasashen Turawan na yamma ya shaida musu cewa Nijeriya ba za ta iya biyan basussukan da suke bi ba, saboda dankaren kudin ruwa, sai dai su yafe kawai!

Kamar yadda Obasanjo ya koka da dankaren kudin ruwan basussukan yamma, shi ma shugaban wata cibiyar binicke kan bunkasa tattalin arziki da ci gaba a zamanance ta Asiya da ke Pakistan, Shakeel Ahmad Ramay ya ce, “Babbar matsalarmu ita ce basussukan da muka ci daga hukumomin kudi na kasashen yamma, Pakistan ba za ta iya biyan su ba saboda basussuka ne masu dankaren kudin ruwa.”

Bayanai daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa kashi uku bisa hudun basussukan da Afirka ke ka-ka-ni-ka-yi da su daga cibiyoyin kudi ne na kasashen duniya amma ba kasar Sin ba.

Shi ya sa mataimakin sakataren kungiyar kawancen Sin da Zambia, Chibeza Mfun ya ce, “idan ma akwai abin da ya fi ci mana tuwo a kwarya a matsayinmu na kasa, shi ne biyu bisa ukun basussukan da ake bin mu. Ba kasar Sin ke bin mu biyu bisa uku ba, masu kawo gudunmawa ne daga kasashen yamma da cibiyoyin kudi.”

Maimakon yamadidi, kamata ya yi Amurka da sauran kasashen yamma su dubi yadda suke bautar da kasashe masu tasowa da kudin ruwan da suke lafta wa basussukan da suke bin su, da yayyafa wa rikicin Ukraine da suka kunna ruwa wanda yake barazana tare da nakasa kasashe masu tasowa. A halin yanzu dai kan mage ya waye, batun yamadidin “Tarkon Bashin Sin”, gidan toka ne da ake son ginawa a tsakiyar teku!

Tarkon Bashin Sin
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.