• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Manoma Mata Sun Bukaci Kara Yawan Kasafin Kudin Aikin Noma

by Abubakar Abba
7 months ago
in Labarai
0
Kananan Manoma Mata Sun Bukaci Kara Yawan Kasafin Kudin Aikin Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma mata a Jihar Ebonyi, sun bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, da su zuba jari mai yawan gaske a fannin noma. Har ila yau, sun yi nuni da cewa; hakan zai taimaka matuka wajen kawo karshen matsalar karancin abinci a fadin kasar.

Manoman sun kara da cewa, kara samun zuba jari a fannin zai kara yawan tattalin arzikin noma zuwa a kalla kashi shida cikin dari.

  • Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma
  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Gonakin Manoma A Zamfara

Sun sanar da haka ne, a taron masu ruwa da tsaki kan kasafin kudi da jihar ta  Ebonyi ta ware wa fannin a 2025.

An gudanar da taron ne, bisa hadakar ma’aikatar aikin noma da kula da albarkatun kasa ta jihar da kuma kwamitin kasafin kudi na jihar tare da kungiyoyin mata na kananan manoma.

Kana, an samu nasarar aiwatar da taron ne tare da goyon bayan kungiyar ‘Actionaid’; wadda ke gudanar da ayyukanta a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

Bugu da kari, manoman sun kuma yi kira ga gwamnati da ta samar da tsare-tsare tare da kafa dokoki a kan yin amfani da magungunan kashe kwari da ke dauke da sinadaran da za su iya shafar kiwon lafiyar manoma.

Kazalika, sun yi kira ga majalisar dokokin jihar da ta tabbatar da an amince da kasafin kudin a kan lokaci da kuma yin amfani da dabarun kara bunkasa noma a jihar.

A cewarsu, yin hakan a kan lokaci; zai taimaka wajen rage yunwa da fatara, musamman don cika yarjejeniyar Maputo/Malabo da aka rattabawa hannu.

Sannan kuma, sun bukaci ‘yan majalisar da su tabbatar da cewa, sun mayar da hankali a fannin aikin noman; domin amfanin al’ummar mazabunsu.

Manoman, sun kuma shawarci ma’aikatar aikin noma ta jihar da hukumomin gwamnatin jihar, da su tabbatar sun fadada tuntuba da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma a yayin wanzar da kasafin kudin na badi.

Sun kuma bukaci a zuba jari na musamman, wajen sama wa manoma mata rance da kuma kayan aikin noma na zamani, musamman don rage yawan asarar da manoman ke yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmersNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi Kan Dabarun Noman Dankalin Turawa

Next Post

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

Related

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

10 minutes ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

2 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

4 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

13 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

15 hours ago
Next Post
Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.