• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Kano Ta Rungumi Ilimin Kimiyya Don Kyautata Rayuwar Jama’a – Kwamishina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta ta rungumar harkokin kimiyya da fahasa, domin kyautata rayuwar dumbin al’ummar da ke fadin jihar ta hanyar bayar da muhimmanci ga harkokin kimiyya da fasaha a jihar.

Kwamishinan Ma’aikatar Kimiyya, fasaha da kere-keren zamani na jihar, Muhammed Tajo Othman, wanda ya jagoranci babban sakatare da daraktocin ma’aikatar zuwa zagayen duba Cibiyar Musulunci ta Kura da Wudil da suke jihar, domin duba injinan wasan kwallon kafa da wasu injinan da aka yi watsi da su.

  • Ganduje Ya Magantu Kan Nasarar Jam’iyyar APC A Kano, Ya Ce Gawuna Zai Zo Wa Kano Da Alheri

Tajo Othman ya ce, Gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta sanya hankali sosai wajen ganin ta yi amfani da harkokin kimiyya da fasaha da kere-kere, domin tabbatar da cewa a halin da ake ciki yanzu na kimiyya da fasaha na taimakawa sosai wajen bukatar ci gaba, don haka jihar ba za ta yi wasa da wannan fanni ko kadan ba.

Kwamishinan ya kara dacewa, ziyarar na kunshe ne da manufar duba halin da injinan suke ciki, domin ganin an bi matakan da suka dace wajen gyara su tare da tabbatar da ganin sun dawo sun ci gaba da aiki yadda ya kamata.

“Akwai shirye-shiryen da ake yi na horas da jami’ai ta yadda za su tafi daidai da zamanin, sannan yanzu haka duniya na tafiya ne tare da kwarewar zamani”, in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Haka zalika, ya bukaci jami’an da aka horas a cibiyoyin da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tabbatar da yin amfani da injinan yadda ake bukata. Sannan ya kuma hore su da su yi amfani da ilimin da suka samu wajen tsayuwa da kafafunsu.

Da suke yin nasu jawabin, mahalarta taron na Kananan Hukumomin da ban da ban sun bayyana cewa, injinan za su iya fitar da balabalan kwallon kafar akalla kimanin guda 100 a kowace rana. Sun kuma kara da cewa, dukkanin Kananan Hukumomin Jihar 44, sun amfani da wadannan cibiyoyi.

Sannan sun kuma roki Gwamnan Jihar, ya samar musu da muhallai na dindindin domin taimaka musu wajen kara jajircewa tare da jan damarar yin aiki yadda ya kamata.

Haka zalika, ababen da kwamishinan ya duba yayin ziyarar tasa sun hada da injin yanka kwallon kafa da jannareto mai girman 15KBA da kuma fatar da ake yin amfani da ita wajen lullebe kwallon da kuma wasu sauran kayayyaki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasahaKimiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Da ‘Yan Sintiri Sun Yi Nasarar Halaka ‘Yan Bindiga A Jihar Kebbi

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Jami’ar Tarayya Ta Gusau Sun Sace Dalibai

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

7 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

12 months ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

'Yan Bindiga Sun Kutsa Kai Jami'ar Tarayya Ta Gusau Sun Sace Dalibai

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.