• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Gas Ya Jefa Al’umma Cikin Duhu Da Matsaloli A Bangaren Lantarki A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
TCN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu sassan Nijeriya sun fada cikin duhu sakamakon karancin iskar gas lamarin da ya kara janyo damuwa da tashin hankali hadi da kara lafta matsaloli kan sha’anin wutar lantarki a Nijeriya.

An rawaito cewa a makon jiya ne gwamnatin Nijeriya da kamfanin rarraba wutar lantarki na Nijeriya suka dauka alhakin karancin samun wutar lantarki a Nijeriya da karancin samun iskar gas a ‘yan makonnin da suka gabata.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mahalarta Ɗaurin Aure 55, Da Kashe Mutane 3 A Katsina
  • Tabbas Philippines Ba Za Ta Cimma Yunkurinta Na Kafa “Karamar Da’Ira” A Tekun Kudancin Sin Ba

Bugu da kari a ‘yan watannin baya, gwamnatin ta kuma daura alhakin karancin samun iskar gas kan rage yawan wutar lantarkin da babban kamfanin samar da wutar lantarki ta Niger Delta Power Holding Campani (NDPHC) ta yi ga kamfanonin rarraba wutar lantarki.

Samar da wutar lantarki a Nijeriya ya dogara ne kan manyan tekun ruwa da layukan gas.

Duk da tsawon shekaru da aka shafe a Nijeriya ana fitar da makuden kudade, har yanzu lamarin wutar lantarki na fuskantar matsalolin rashin wadatan ‘yan kasa kuma al’umma sun dogara sosai wajen amfani da wutar lantarki wajen gudanar da harkokin rayuwa da daman gaske.

Labarai Masu Nasaba

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

A karshen shekarar 2023 hukumomin da ke sanya ido kan harkoki wuta da NERC sun cewa karancin gas ne babban matsalar da ke shafan lamarin harkokin lantarki a Nijeriya.

Wannan matsalar na zuwa ne a daidai lokacin da Nijeriya ta kasance na da arzikin gas tiriliyan 208.83 kwatankwacin kaso 33 na adadin gas da Afrika ke da shi, a cewar babban jami’in gudanarwar NUPRC, Gbenga Komolafe.

Kamar sauran bangarori a Nijeriya, masana’antar samar da wutar lantarki na fuskantar tulin matsalolin da suke kawo tsaiko ga cigabanta.

Da ya ke ganawa da wata kafa a ranar Litinin, Bokaji Tunji, babban mai bada shawara kan harkokin yada labarai wa ministan lantarki, Adebayo Adebalubu, ya ce, gwamnatin tarayya ta hannanta lamarin shawo kan matsalar karancin gas ga GenCos.

A cewarsa, tunin gwamnatin ta fara tuntubar masu ruwa da tsaki domin shawo kan matsalolin ciki har biyan basukan da GenCos ke bi.

“Ministan yana iyaka bakin kokarinsa wajen ganin an shawo kan matsalar, ciki har da biyan basukan da kamfanoni GenCos ke biya da sauran masu ruwa da tsaki.”

“Ina tabbatar muku ministan zai shawo kan matsalar karancin gas zuwa ga kamfanonin da ke rarraba gas din,” ya shaida.

Kazalika, sakataren kamfanonin lantarki, APGC, Joy Ogaji, ta ce, ba ta da masaniyar cewa gwamnatin tarayya na tattaunawa da GenCos domin shawo kan matsalolin gas.

Ogaji, ta ce, da yiyuwar gwamnatin ta tsara matakan da za a bi wajen shawo kan matsalolin da ke addabar kamfanonin samar da wutar lantarki, NESI.

Shi kuma Kunle Olubiyo, shugaban NCPN, ya daura laifin ga gwamnati, ya ce gwamnati ne kawai za ta yi abubuwan da suka dace wajen samun mafita ga matsalolin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karancin lantarkiTCN
ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Sanar Da Kuɗin Kujerar Hajjin Bana Duk Da Hauhawar Farashin Dala

Next Post

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

Related

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

22 minutes ago
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

2 hours ago
Kwale-kwale
Labarai

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

4 hours ago
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

6 hours ago
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

15 hours ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

15 hours ago
Next Post
Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

Jihar Bauchi Ta Lashe Lambar Yabon Kwazo A Bangaren Mai Da Iskar Gas

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Kwale-kwale

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

October 6, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.