• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara

by Muhammad
1 year ago
in Dausayin Musulunci, Manyan Labarai
0
Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, ya ce haddar Alkur’ani mai girma da karatun Alkur’ani za su taimaka matuka gaya wajen bunkasar kwakwalwa ga masu karatu musamman matasa.

Ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su tabbatar da karantawa da haddar hadisan Annabi (S.A.W.).

  • Ya Sace Katan 20 Na Alkur’ani Da Hadisai A Kwara
  • An Bizne Gawar Jakadan Nijeriya Na Kasar Faransa A Jihar Kwara

Gwamnan ya yi wannan jawabi a ranar Lahadin da ta gabata a garin Ilorin a wajen rufe gasar karatun Alkur’ani da Hadisi da ofishin kula da al’adu na ofishin jakadancin Saudiyya da ke Abuja da kuma Cibiyar Da’awah da Bincike ta As-Sunnah da ke Ilorin suka shirya a Jihar Kwara.

Gwamnan ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Farfesa Mamman Saba Jibril.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa gasar ta kunshi bangare shida, kowanne bangare ya kunshi hazikan dalibai da mahaddata Alkur’ani da Hadisi.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Manyan daliban da aka gwabza da su a wannan rana sun hada da Abdulrahman Ismail da Ahmad Abdulsalam da Abdullateef Zakariyya da Khadijah Ajijolakewu da Zainab AbdulGafar da Naeem Abdulsalam da Usman Ayinde da Kamaldeen Suleiman da Abdulmajeed Abdullateef.

Sauran sun hada da Ahmad Abdulazeez da Muslimah Abdullateef da Sofiyullahi Murtadha da Maryam Abdulkareem da Maiyaki Muktar; Salimah Abubakar da Aisha Abdulrahman da Zainab Abubakar da kuma Ali Muhammad.

Gwamnan ya ce, ya zama wajibi ga Musulmi musamman matasa su ci gaba da neman ilimin Alkur’ani da Hadisi, tare da haddace su don ciyar da addinin Musulunci gaba da kuma jagorantar rayuwarsu.

AbdulRazaq ya bayyana littafin a matsayin tushe na dukkan ilimi, ya kuma dora wa masu imani da su sadaukar da kansu wajen karatu da nazarinsa akai-akai, yayin da yake taya wadanda suka shirya gasar da kuma wadanda suka yi nasara daban-daban murnar samun nasarar gudanar da gasar.

Ya kuma yi alkawarin gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayi da zai ba da damar zaman lafiya da a tsakanin mabiya addinai a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al-qur'aniGwamnatin KwaraKwaraMusabaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Kwallon Hannu Ta Afirika: Nijeriya Ta Doke Kasar Kenya

Next Post

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

2 hours ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

24 hours ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

1 day ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

2 days ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

2 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

3 days ago
Next Post
Gwamnan Kaduna, Uba Sani, yayi ziyarar duba aikin gina gidajen marayu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke ginawa a Kaduna

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.