• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara

by Muhammad
2 years ago
in Dausayin Musulunci, Manyan Labarai
0
Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, ya ce haddar Alkur’ani mai girma da karatun Alkur’ani za su taimaka matuka gaya wajen bunkasar kwakwalwa ga masu karatu musamman matasa.

Ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su tabbatar da karantawa da haddar hadisan Annabi (S.A.W.).

  • Ya Sace Katan 20 Na Alkur’ani Da Hadisai A Kwara
  • An Bizne Gawar Jakadan Nijeriya Na Kasar Faransa A Jihar Kwara

Gwamnan ya yi wannan jawabi a ranar Lahadin da ta gabata a garin Ilorin a wajen rufe gasar karatun Alkur’ani da Hadisi da ofishin kula da al’adu na ofishin jakadancin Saudiyya da ke Abuja da kuma Cibiyar Da’awah da Bincike ta As-Sunnah da ke Ilorin suka shirya a Jihar Kwara.

Gwamnan ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Farfesa Mamman Saba Jibril.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa gasar ta kunshi bangare shida, kowanne bangare ya kunshi hazikan dalibai da mahaddata Alkur’ani da Hadisi.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Manyan daliban da aka gwabza da su a wannan rana sun hada da Abdulrahman Ismail da Ahmad Abdulsalam da Abdullateef Zakariyya da Khadijah Ajijolakewu da Zainab AbdulGafar da Naeem Abdulsalam da Usman Ayinde da Kamaldeen Suleiman da Abdulmajeed Abdullateef.

Sauran sun hada da Ahmad Abdulazeez da Muslimah Abdullateef da Sofiyullahi Murtadha da Maryam Abdulkareem da Maiyaki Muktar; Salimah Abubakar da Aisha Abdulrahman da Zainab Abubakar da kuma Ali Muhammad.

Gwamnan ya ce, ya zama wajibi ga Musulmi musamman matasa su ci gaba da neman ilimin Alkur’ani da Hadisi, tare da haddace su don ciyar da addinin Musulunci gaba da kuma jagorantar rayuwarsu.

AbdulRazaq ya bayyana littafin a matsayin tushe na dukkan ilimi, ya kuma dora wa masu imani da su sadaukar da kansu wajen karatu da nazarinsa akai-akai, yayin da yake taya wadanda suka shirya gasar da kuma wadanda suka yi nasara daban-daban murnar samun nasarar gudanar da gasar.

Ya kuma yi alkawarin gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayi da zai ba da damar zaman lafiya da a tsakanin mabiya addinai a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al-qur'aniGwamnatin KwaraKwaraMusabaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Kwallon Hannu Ta Afirika: Nijeriya Ta Doke Kasar Kenya

Next Post

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

Related

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

1 hour ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

2 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

3 hours ago
Kamfani
Manyan Labarai

‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.

17 hours ago
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

23 hours ago
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
Manyan Labarai

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

1 day ago
Next Post
Gwamnan Kaduna, Uba Sani, yayi ziyarar duba aikin gina gidajen marayu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke ginawa a Kaduna

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.