• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara

by Muhammad
1 year ago
in Dausayin Musulunci, Manyan Labarai
0
Karatun Al-ƙur’ani Da Hadda Ce Shi, Yana Taimawa Ginuwar Ƙwaƙwalwa -Gwamnan Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, ya ce haddar Alkur’ani mai girma da karatun Alkur’ani za su taimaka matuka gaya wajen bunkasar kwakwalwa ga masu karatu musamman matasa.

Ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su tabbatar da karantawa da haddar hadisan Annabi (S.A.W.).

  • Ya Sace Katan 20 Na Alkur’ani Da Hadisai A Kwara
  • An Bizne Gawar Jakadan Nijeriya Na Kasar Faransa A Jihar Kwara

Gwamnan ya yi wannan jawabi a ranar Lahadin da ta gabata a garin Ilorin a wajen rufe gasar karatun Alkur’ani da Hadisi da ofishin kula da al’adu na ofishin jakadancin Saudiyya da ke Abuja da kuma Cibiyar Da’awah da Bincike ta As-Sunnah da ke Ilorin suka shirya a Jihar Kwara.

Gwamnan ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Farfesa Mamman Saba Jibril.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa gasar ta kunshi bangare shida, kowanne bangare ya kunshi hazikan dalibai da mahaddata Alkur’ani da Hadisi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Manyan daliban da aka gwabza da su a wannan rana sun hada da Abdulrahman Ismail da Ahmad Abdulsalam da Abdullateef Zakariyya da Khadijah Ajijolakewu da Zainab AbdulGafar da Naeem Abdulsalam da Usman Ayinde da Kamaldeen Suleiman da Abdulmajeed Abdullateef.

Sauran sun hada da Ahmad Abdulazeez da Muslimah Abdullateef da Sofiyullahi Murtadha da Maryam Abdulkareem da Maiyaki Muktar; Salimah Abubakar da Aisha Abdulrahman da Zainab Abubakar da kuma Ali Muhammad.

Gwamnan ya ce, ya zama wajibi ga Musulmi musamman matasa su ci gaba da neman ilimin Alkur’ani da Hadisi, tare da haddace su don ciyar da addinin Musulunci gaba da kuma jagorantar rayuwarsu.

AbdulRazaq ya bayyana littafin a matsayin tushe na dukkan ilimi, ya kuma dora wa masu imani da su sadaukar da kansu wajen karatu da nazarinsa akai-akai, yayin da yake taya wadanda suka shirya gasar da kuma wadanda suka yi nasara daban-daban murnar samun nasarar gudanar da gasar.

Ya kuma yi alkawarin gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayi da zai ba da damar zaman lafiya da a tsakanin mabiya addinai a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al-qur'aniGwamnatin KwaraKwaraMusabaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Kwallon Hannu Ta Afirika: Nijeriya Ta Doke Kasar Kenya

Next Post

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

Related

Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

19 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

1 day ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

2 days ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

2 days ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

3 days ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

3 days ago
Next Post
Gwamnan Kaduna, Uba Sani, yayi ziyarar duba aikin gina gidajen marayu da gidauniyar tallafi ta Qatar ke ginawa a Kaduna

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.