ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

by Sadiq
10 months ago
Jigawa

Rundunar ’Yansandan Jihar Jigawa ta kama mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da wasu mutane 156 bisa laifuka daban-daban cikin watanni biyu da suka gabata.

Kwamishinan ’Yansandan jihar, CP Dahiru Muhammad ne, ya shaida wa manema labarai cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama, Adamu Musa mai shekara 47 daga unguwar Yalwawa a Dutse, shugaban masu garkuwa da mutane ne.

  • Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
  • Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Ana zargin ya yi garkuwa da mutane huɗu daga ƙaramar hukumar Sumaila ta Jihar Kano, inda ya tsare su a ƙauyen Baranda na ƙaramar  hukumar Dutse.

ADVERTISEMENT

Ya saki mutanen ne bayan ya karɓi kuɗin fansa har Naira miliyan takwas da babur ɗaya wanda darajarsa ta kai Naira miliyan ɗaya.

Haka kuma, a ranar 29 ga watan Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 3 na rana, ’yansanda tare da jami’an sa-kai sun kama wani da ake zargi da garkuwa da mutane da fashi makami ne.

LABARAI MASU NASABA

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Wanda aka kama sunansa iro Garba mai shekaru 25 daga Zangwaye Fulani a ƙaramar hukumar Ajingi a Jihar Kano.

Ya amsa cewa shi da wasu mutane huɗu sun yi garkuwa da mutane a Kano, Jigawa da Bauchi.

An kuma samu rigunan sojoji guda uku a hannunsa.

Kwamishinan ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin kama sauran mutane huɗun da ake zargi da hannu a garkuwar da ta faru a Sumaila, da ke Jihar Kano.

A wani lamari kuma, ’yansanda sun kama mutane huɗu da ake zargi da fasa shago a ƙaramar hukumar Malam Madori.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Nuhu Yusif Saleh (19), Hassan Ibrahim (19), da Nura Musa (22).

An ƙwato akwati mai ɗauke da kuɗi Naira 870,000, abun cajin waya guda biyu, na’urar PoS, wayoyi guda 20, da lasifiƙa daga hannunsu.

Jimillar mutanen da aka kama a cikin watanni biyu sun kai 156 bisa laifuka daban-daban, ciki har da safarar makamai, fashi da makami, kisan kai, fyaɗe, lalata kayan gwamnati, fataucin miyagun ƙwayoyi da sata.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da bindiga AK-47 guda biyu, motoci guda uku, adaidaita sahu guda ɗaya, wayoyi guda 23, shanun sata guda 14, da kuma miyagun ƙwayoyi kamar tramadol, diazepam, exol, tabar wiwi, da sauransu.

CP Muhammad ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka da kuma safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin Jihar Jigawa.

MASU ALAKA

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
Manyan Labarai

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
Manyan Labarai

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Next Post
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Jigawa

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.