ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

by Sadiq
11 months ago
Jigawa

Rundunar ’Yansandan Jihar Jigawa ta kama mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da wasu mutane 156 bisa laifuka daban-daban cikin watanni biyu da suka gabata.

Kwamishinan ’Yansandan jihar, CP Dahiru Muhammad ne, ya shaida wa manema labarai cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama, Adamu Musa mai shekara 47 daga unguwar Yalwawa a Dutse, shugaban masu garkuwa da mutane ne.

  • Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
  • Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Ana zargin ya yi garkuwa da mutane huɗu daga ƙaramar hukumar Sumaila ta Jihar Kano, inda ya tsare su a ƙauyen Baranda na ƙaramar  hukumar Dutse.

ADVERTISEMENT

Ya saki mutanen ne bayan ya karɓi kuɗin fansa har Naira miliyan takwas da babur ɗaya wanda darajarsa ta kai Naira miliyan ɗaya.

Haka kuma, a ranar 29 ga watan Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 3 na rana, ’yansanda tare da jami’an sa-kai sun kama wani da ake zargi da garkuwa da mutane da fashi makami ne.

LABARAI MASU NASABA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

Wanda aka kama sunansa iro Garba mai shekaru 25 daga Zangwaye Fulani a ƙaramar hukumar Ajingi a Jihar Kano.

Ya amsa cewa shi da wasu mutane huɗu sun yi garkuwa da mutane a Kano, Jigawa da Bauchi.

An kuma samu rigunan sojoji guda uku a hannunsa.

Kwamishinan ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin kama sauran mutane huɗun da ake zargi da hannu a garkuwar da ta faru a Sumaila, da ke Jihar Kano.

A wani lamari kuma, ’yansanda sun kama mutane huɗu da ake zargi da fasa shago a ƙaramar hukumar Malam Madori.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Nuhu Yusif Saleh (19), Hassan Ibrahim (19), da Nura Musa (22).

An ƙwato akwati mai ɗauke da kuɗi Naira 870,000, abun cajin waya guda biyu, na’urar PoS, wayoyi guda 20, da lasifiƙa daga hannunsu.

Jimillar mutanen da aka kama a cikin watanni biyu sun kai 156 bisa laifuka daban-daban, ciki har da safarar makamai, fashi da makami, kisan kai, fyaɗe, lalata kayan gwamnati, fataucin miyagun ƙwayoyi da sata.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da bindiga AK-47 guda biyu, motoci guda uku, adaidaita sahu guda ɗaya, wayoyi guda 23, shanun sata guda 14, da kuma miyagun ƙwayoyi kamar tramadol, diazepam, exol, tabar wiwi, da sauransu.

CP Muhammad ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka da kuma safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin Jihar Jigawa.

MASU ALAKA

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Next Post
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.