ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Nagudu

Tsohon mawakin soyayya a masana’antar Kannywood wanda ya yi shura a fagen wakokin soyayya a shekarun da suka gabata, Ahmed Mahmud Abdulkadir ko kuma Mahmud Nagudu kamar yadda aka fi saninsa ya karyata wadanda suka ce ya bayyana wakokin soyayya a matsayin haramun, inda ya tabbatar da cewar wasu dalilai ne suka sa ya daina wakokin soyayya ba don suna da haramci ba kamar yadda wasu suke fadi.

 

Mahmud a wata hira da ya yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show ya yi karin haske a kan wasu daga cikin dalilan da suka janyo ya daina yin wakokin soyayya da aka sanshi dasu a baya,wanda daga ciki akwai karewar basira a wannan fanni na wakokin soyayya kamar yadda ya bayyana.

ADVERTISEMENT
  • Sakataren Kudi Na Ƙungiyar Ɗalibai Shiyya Ta Ɗaya Ya Nemi A Shiga Zanga-zanga
  • In Dai Ina Raye, Ba Ni Da Wani Aiki Da Ya Wuce Buga Littattafai – Gidan Dabino

Da farko dai babu inda nace waka haramun ne hasali ma har yanzu ina yin wakoki sai dai ba na soyayya ba kamar yadda aka fi sani na dasu, domin kuwa yanzu shekaruna sun ja kuma ayyuka sun kara yi mani yawa,sannan kuma ina ganin kamar basira ta ta kare a wannan fanni na wakokin soyayya,don ba zai yiwu ace kullum babu abin da zaka dinga fadi a waka ba illa kalmar so kawai, hakan yasa nike ganin kamar babu wani abu wanda na sani a soyayya da ban bayyana shi a cikin wakokin da nayi a baya ba, in ji Mahmud.

 

LABARAI MASU NASABA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Ya ci gaba da cewar yanzu da nake wakoki na yabon Manzon Allah (S A W) akwai bukatar in samu ilimi dangane da wannan Manzo na Allah ba kawai in dinga rera kalaman da suka burge ni ba,amma ita wakar soyayya zaka iya saka duk wani abu da ya zo maka a rayuwa ko kuma ka sani dangane da soyayya a cikin wakokinka ka baiwa mutane kuma a yaba maka ba kamar bege ba.

 

Da yake amsa tambaya a kan irin sana’ar da yake yi yanzu bayan barin wakokin Kannywood sai Mahmud ya ce kasuwanci yake yi a yanzu ko kuma buga buga kamar yadda bahaushe yake fadi,sannan kuma maganar barin masana’antar Kannywood wannan ba gaskiya bane domin kuwa har yanzu yana abin arziki da masu shirya fina finai da saurnan jarumai a masana’antar ta Kannywood.

 

Da yake magana a kan matsalolin da yake tunanin sun yi wa masana’antar Kannywood katutu da kuma hanyoyin da zaa bi wajen magance su Mahmud ya ce, babbar matsalar wannan masana’antar ba wani abu ba ne illa rashin kofa ma’ana duk wani wanda yake son shigowa zai ita shigowa ba tareda an san ya shigo ba balantana a tambayeshi wanene shi kokuma daga ina ya fito.

 

Amma matukar za a dauki mataki a kan irin wadannan mutane masu yi wa Kannywood shigar kutse a dinga tantance su, a bincikesu daga ina suka fito minene sana’oinsu kafin shigowa Kannywood da sauran tambayoyi kafin a basu damar shigowa kokuma mallakar shaidar zama ‘ya’yan Kannywood to za a samu saukin shigowar wadanda suke da karancin tarbiyya da zasu janyowa masana’antar zagi kokuma bacin suna a wajen al’umma.

 

Dangane da nasarorin da Mahmud ya samu a Kannywood kuwa, tsohon mawakin ya bayyana dimbin nasarorin da ya samu da suka hada da haduwa da manya kuma nagartattun mutane da kuma sauran arzika,daukaka da kuma tarin masoya da yace Allah ya bashi a tsawon shekarun da ya kwashe a masana’antar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA
Nishadi

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu
Nishadi

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
Nishadi

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Muhimmin Sakon Kwankwaso Ga 'Yan Nijeriya Kan Shirin Zanga-zanga 

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.