• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karewar Basira A Wakokin Soyayya Ta Sa Na Daina Yin Su – Mahmud Nagudu

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Nagudu

Tsohon mawakin soyayya a masana’antar Kannywood wanda ya yi shura a fagen wakokin soyayya a shekarun da suka gabata, Ahmed Mahmud Abdulkadir ko kuma Mahmud Nagudu kamar yadda aka fi saninsa ya karyata wadanda suka ce ya bayyana wakokin soyayya a matsayin haramun, inda ya tabbatar da cewar wasu dalilai ne suka sa ya daina wakokin soyayya ba don suna da haramci ba kamar yadda wasu suke fadi.

 

Mahmud a wata hira da ya yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show ya yi karin haske a kan wasu daga cikin dalilan da suka janyo ya daina yin wakokin soyayya da aka sanshi dasu a baya,wanda daga ciki akwai karewar basira a wannan fanni na wakokin soyayya kamar yadda ya bayyana.

  • Sakataren Kudi Na Ƙungiyar Ɗalibai Shiyya Ta Ɗaya Ya Nemi A Shiga Zanga-zanga
  • In Dai Ina Raye, Ba Ni Da Wani Aiki Da Ya Wuce Buga Littattafai – Gidan Dabino

Da farko dai babu inda nace waka haramun ne hasali ma har yanzu ina yin wakoki sai dai ba na soyayya ba kamar yadda aka fi sani na dasu, domin kuwa yanzu shekaruna sun ja kuma ayyuka sun kara yi mani yawa,sannan kuma ina ganin kamar basira ta ta kare a wannan fanni na wakokin soyayya,don ba zai yiwu ace kullum babu abin da zaka dinga fadi a waka ba illa kalmar so kawai, hakan yasa nike ganin kamar babu wani abu wanda na sani a soyayya da ban bayyana shi a cikin wakokin da nayi a baya ba, in ji Mahmud.

 

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Ya ci gaba da cewar yanzu da nake wakoki na yabon Manzon Allah (S A W) akwai bukatar in samu ilimi dangane da wannan Manzo na Allah ba kawai in dinga rera kalaman da suka burge ni ba,amma ita wakar soyayya zaka iya saka duk wani abu da ya zo maka a rayuwa ko kuma ka sani dangane da soyayya a cikin wakokinka ka baiwa mutane kuma a yaba maka ba kamar bege ba.

 

Da yake amsa tambaya a kan irin sana’ar da yake yi yanzu bayan barin wakokin Kannywood sai Mahmud ya ce kasuwanci yake yi a yanzu ko kuma buga buga kamar yadda bahaushe yake fadi,sannan kuma maganar barin masana’antar Kannywood wannan ba gaskiya bane domin kuwa har yanzu yana abin arziki da masu shirya fina finai da saurnan jarumai a masana’antar ta Kannywood.

 

Da yake magana a kan matsalolin da yake tunanin sun yi wa masana’antar Kannywood katutu da kuma hanyoyin da zaa bi wajen magance su Mahmud ya ce, babbar matsalar wannan masana’antar ba wani abu ba ne illa rashin kofa ma’ana duk wani wanda yake son shigowa zai ita shigowa ba tareda an san ya shigo ba balantana a tambayeshi wanene shi kokuma daga ina ya fito.

 

Amma matukar za a dauki mataki a kan irin wadannan mutane masu yi wa Kannywood shigar kutse a dinga tantance su, a bincikesu daga ina suka fito minene sana’oinsu kafin shigowa Kannywood da sauran tambayoyi kafin a basu damar shigowa kokuma mallakar shaidar zama ‘ya’yan Kannywood to za a samu saukin shigowar wadanda suke da karancin tarbiyya da zasu janyowa masana’antar zagi kokuma bacin suna a wajen al’umma.

 

Dangane da nasarorin da Mahmud ya samu a Kannywood kuwa, tsohon mawakin ya bayyana dimbin nasarorin da ya samu da suka hada da haduwa da manya kuma nagartattun mutane da kuma sauran arzika,daukaka da kuma tarin masoya da yace Allah ya bashi a tsawon shekarun da ya kwashe a masana’antar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Muhimmin Sakon Kwankwaso Ga 'Yan Nijeriya Kan Shirin Zanga-zanga 

LABARAI MASU NASABA

IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.