• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karrama Sojojinmu Da Suka Sadaukar Da Kai Don Ɗorewar Nijeriya

by Leadership Hausa
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Karrama Sojojinmu Da Suka Sadaukar Da Kai Don Ɗorewar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk ranar 15 ga watan Janairu na kowace shekara ne, a Nijeriya, ake gudanar da bikin tunawa da zagayowar ranar dakarun sojujin Nijeriya  mazansu da matansu, ‘yan mazan jiya.

A saboda haka ne, yana da matukar mahammianci mu yi waiwaye kan irin sadaukarwar da suka yi ta rayuwarsu, wajen tabbatar da zaman lafiya da hadin kan kasar, musamman ma idan aka yi la’akari da cewa, sun fafata yakin duniya na daya da na biyu da kuma a lokacin yakin basasar Nijeriya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

Ana iya tunawa, kasar Ingila ce, ta reni Nijeriya ta kuma bata ‘yancin kai, a baya ana kara tunawa da zagayowar ranar ce, a ranar 11 na kowane watan Nuwamba, musamman ma domin tuna kawo karshen yakin duniya na farko

Sai dai kuma, bayan da waccen Gwamnatin mulkin soji ta samu galaba a kan dakarun sojojin masu yunkurin kafa kasar Biyafara a ranar 15 ga watan Janairun 1970, aka sauya ranar da gudanar da bikin daga cikin Kalandar kasashen renon Ingila wato Commonwealth, zuwa ranar 15 ga watan Janairun domin, a rinka tunawa da yakin na basasa.

Shekaru aru-aru, dakarun sojojin mu, sun sadaukar da rayukansu wajen kare karfin ikon Nijeriya, rayukan ‘yan kasar,  don tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaba da wanzuwar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Kazalika ma, sadaukar da kansu da kwarin gwiwarsu na fuskantar dukkanin wani hadarin yaki, wanda hakan ya sanya aka ci gaba da nuna godiya a gare su, da  kuma girmama su, a daukacin fadin kasar mu.

Hakan ta sa abin ya zama mana wajibi, mu ci gaba da tuna su da kuma girmama su, la’akari da sadaukar da kan da suka yi ga kasar mu.

Hadurun da suka fuskanta, a zahirance suke, in aka tuna da yadda suka rasa rayukansu, wajen yakar ‘yan ta’adda da sauran masu aikata manyan laifuka, da suka zamo barazana, ga tsaron kasar.

Amma a nan, tunanin mu, ya karkata ne, zuwa ga iyalansu da suka rasu suka bari, abokan arzikinsu da kuma yankunan da suka fito.

Bisa sadaukar da rayukansu da suka yi ne, hakan ya sanya muka ci gaba da zama a cikin zaman lafiya muka kuma ci gaba da gudanar da ayyukansu, na yau da kullum.

A saboda haka ne, akwai babban bashi da yake a kanmu, na ci gaba da tunawa da su, tare da kuma girmama su.

A yayin da muke gudana da bikin tuna su, ya zamar mana wajibi mu taimakawa sauran dakarun ‘yan mazan jiya da ke raye da kuma sauran dakarun da a yau, suke ci gaba da nauyin ba  Nijeriya kariya.

Bugu da kari dakarun namu suna ci gaba dayin aiki tukuru wajen tunkarar dukkan wata barazana daga wurin ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji, masu satar danyen mai da sauran masu aikata manyan laifuka, a kasar.

Abin jin dadi ne, matuka, musamman irin dimbin ci gaban da ake ci gaba da samu, musamman yadda, rundunar tsaron kasar ta ruwaito cewa, dakarunta da ta tura masu dakile aikata ta’addanci, a wasu ayyukan da suka kaddamar, sun kashe ‘yan ta’adda 109, tare da kuma cafke wasu 81 a makon farko na 2025.

Daraktan sashen yada labarai na rundunar Manjo Janar Buba Edward, ya sanar da cewa, “A cikin makon dakarun sun hallaka ‘yan ta’adda 109 tare da kama wasu 81 da kuma ceto wasu mutanen da aka yi garkuwa da su 43.”

Sai dai, a bisa ra’ayin wannan jaridar, duk a wannan dimbin nasarorin da aka samu, akwai sauran manyan kalubale.

Wasu rahotannin suna bayyana cewa, akalla mutane 77 ne, aka kashe tare da kuma yin garkuwa da mutane 43, hakan ya biyo bayan hare-hare da aka kai daban daban a jihohi 10, a cikin mako biyu kacal, da suka wuce.

An kuma kone gidaje da dama, tare da tarwatsa mutane sama da 1,000, daga matsugunansu.

Bugu da kari kuma wasu dakarun soji shida, sun rasa rayukansu, a wani harin na ‘yan ta’adda, a ranar 4 ga watan Janairu 2025.

Sun rasa rayukansu ne, a yayin da maharan suka kai hari a sansanin soja da ke a Sabon Gida, Damboa a jihar Borno.

Bayan kai wannan harin, Shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayar da umarnin da a gudanar da cikakken bincike, tare da kuma yabawa rundunar sojojin kasar kan daukar matakin gaggawa da ta yi, musamman wajen kai hare-hare da Jiragen yaki na sama a kan sansanin ‘yan ta’adda, wanda hakan ya janyo aka kashe su  da dama.

Dole ne mu rinka bai wa dakarun sojojin mu kariyar da ta kamata da kuma kulawa da jin dadinsu da walwalarsu da kula da kiwon lafiyarsu tare da kuma biyan bukatun  iyalansu.

Jajirtattun sojojin da suka dawo daga fagen daga/fama,dole ne a samar masu da gidaje, samar masu da damar samun daukar aiki, domin a karrama su, bisa gudunmawar da suka bayar ta sadaukar da kansu,wajen dorewar tsaro da wanzuwar kasar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

1 hour ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

12 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

16 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

17 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.