• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karrama Sojojinmu Da Suka Sadaukar Da Kai Don Ɗorewar Nijeriya

by Leadership Hausa
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Karrama Sojojinmu Da Suka Sadaukar Da Kai Don Ɗorewar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk ranar 15 ga watan Janairu na kowace shekara ne, a Nijeriya, ake gudanar da bikin tunawa da zagayowar ranar dakarun sojujin Nijeriya  mazansu da matansu, ‘yan mazan jiya.

A saboda haka ne, yana da matukar mahammianci mu yi waiwaye kan irin sadaukarwar da suka yi ta rayuwarsu, wajen tabbatar da zaman lafiya da hadin kan kasar, musamman ma idan aka yi la’akari da cewa, sun fafata yakin duniya na daya da na biyu da kuma a lokacin yakin basasar Nijeriya.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

Ana iya tunawa, kasar Ingila ce, ta reni Nijeriya ta kuma bata ‘yancin kai, a baya ana kara tunawa da zagayowar ranar ce, a ranar 11 na kowane watan Nuwamba, musamman ma domin tuna kawo karshen yakin duniya na farko

Sai dai kuma, bayan da waccen Gwamnatin mulkin soji ta samu galaba a kan dakarun sojojin masu yunkurin kafa kasar Biyafara a ranar 15 ga watan Janairun 1970, aka sauya ranar da gudanar da bikin daga cikin Kalandar kasashen renon Ingila wato Commonwealth, zuwa ranar 15 ga watan Janairun domin, a rinka tunawa da yakin na basasa.

Shekaru aru-aru, dakarun sojojin mu, sun sadaukar da rayukansu wajen kare karfin ikon Nijeriya, rayukan ‘yan kasar,  don tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaba da wanzuwar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Kazalika ma, sadaukar da kansu da kwarin gwiwarsu na fuskantar dukkanin wani hadarin yaki, wanda hakan ya sanya aka ci gaba da nuna godiya a gare su, da  kuma girmama su, a daukacin fadin kasar mu.

Hakan ta sa abin ya zama mana wajibi, mu ci gaba da tuna su da kuma girmama su, la’akari da sadaukar da kan da suka yi ga kasar mu.

Hadurun da suka fuskanta, a zahirance suke, in aka tuna da yadda suka rasa rayukansu, wajen yakar ‘yan ta’adda da sauran masu aikata manyan laifuka, da suka zamo barazana, ga tsaron kasar.

Amma a nan, tunanin mu, ya karkata ne, zuwa ga iyalansu da suka rasu suka bari, abokan arzikinsu da kuma yankunan da suka fito.

Bisa sadaukar da rayukansu da suka yi ne, hakan ya sanya muka ci gaba da zama a cikin zaman lafiya muka kuma ci gaba da gudanar da ayyukansu, na yau da kullum.

A saboda haka ne, akwai babban bashi da yake a kanmu, na ci gaba da tunawa da su, tare da kuma girmama su.

A yayin da muke gudana da bikin tuna su, ya zamar mana wajibi mu taimakawa sauran dakarun ‘yan mazan jiya da ke raye da kuma sauran dakarun da a yau, suke ci gaba da nauyin ba  Nijeriya kariya.

Bugu da kari dakarun namu suna ci gaba dayin aiki tukuru wajen tunkarar dukkan wata barazana daga wurin ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji, masu satar danyen mai da sauran masu aikata manyan laifuka, a kasar.

Abin jin dadi ne, matuka, musamman irin dimbin ci gaban da ake ci gaba da samu, musamman yadda, rundunar tsaron kasar ta ruwaito cewa, dakarunta da ta tura masu dakile aikata ta’addanci, a wasu ayyukan da suka kaddamar, sun kashe ‘yan ta’adda 109, tare da kuma cafke wasu 81 a makon farko na 2025.

Daraktan sashen yada labarai na rundunar Manjo Janar Buba Edward, ya sanar da cewa, “A cikin makon dakarun sun hallaka ‘yan ta’adda 109 tare da kama wasu 81 da kuma ceto wasu mutanen da aka yi garkuwa da su 43.”

Sai dai, a bisa ra’ayin wannan jaridar, duk a wannan dimbin nasarorin da aka samu, akwai sauran manyan kalubale.

Wasu rahotannin suna bayyana cewa, akalla mutane 77 ne, aka kashe tare da kuma yin garkuwa da mutane 43, hakan ya biyo bayan hare-hare da aka kai daban daban a jihohi 10, a cikin mako biyu kacal, da suka wuce.

An kuma kone gidaje da dama, tare da tarwatsa mutane sama da 1,000, daga matsugunansu.

Bugu da kari kuma wasu dakarun soji shida, sun rasa rayukansu, a wani harin na ‘yan ta’adda, a ranar 4 ga watan Janairu 2025.

Sun rasa rayukansu ne, a yayin da maharan suka kai hari a sansanin soja da ke a Sabon Gida, Damboa a jihar Borno.

Bayan kai wannan harin, Shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayar da umarnin da a gudanar da cikakken bincike, tare da kuma yabawa rundunar sojojin kasar kan daukar matakin gaggawa da ta yi, musamman wajen kai hare-hare da Jiragen yaki na sama a kan sansanin ‘yan ta’adda, wanda hakan ya janyo aka kashe su  da dama.

Dole ne mu rinka bai wa dakarun sojojin mu kariyar da ta kamata da kuma kulawa da jin dadinsu da walwalarsu da kula da kiwon lafiyarsu tare da kuma biyan bukatun  iyalansu.

Jajirtattun sojojin da suka dawo daga fagen daga/fama,dole ne a samar masu da gidaje, samar masu da damar samun daukar aiki, domin a karrama su, bisa gudunmawar da suka bayar ta sadaukar da kansu,wajen dorewar tsaro da wanzuwar kasar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

Related

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

14 hours ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

16 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

18 hours ago
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
Manyan Labarai

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

21 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

1 day ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

2 days ago
Next Post
Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

Badakalar Tashar Lantarkin Mambilla: Buhari Da Obasanjo Sun Ba Da Shaida A Kotun Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.