• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karya Fure Take: Shigowar Baki Kasar Sin, Zai Karyata Karairayin Da Ake Yadawa Game Da Kasar

by Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Karya Fure Take: Shigowar Baki Kasar Sin, Zai Karyata Karairayin Da Ake Yadawa Game Da Kasar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya ce tsakanin watan Janairu da Yulin bana, adadin mutanen da suka yi shige da fice ta tashoshin shigowa kasar Sin sun kai miliyan 341, wanda ya karu da kaso 62.34 bisa dari kan na makamancin lokacin a bara.

 

Tabbas ci gaban da aka samu a watannin 7, na da nasaba da managartan manufofi da matakan da gwamnatin kasar Sin ke aiwatarwa. Misali, manufar shiga kasar ba tare da shaidar biza ba ga wasu kasashe da kyakkyawan tsare-tsaren sufuri da fadada bude kofa da ma ci gaban da take samu a dukkan fannoni, da uwa-uba tsaro da zaman lafiya, wasu abubuwa ne daga cikin dalilan da suka sanya ake samun karuwar masu ziyartar kasar.

  • Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kai Wani Sabon Matsayi
  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe

Gani ya kori ji! Ta hanyar shigowa kasar Sin da ma fasahohin da zamani ya kawo mana, baki za su iya ganewa idanunsu ainihin kasar Sin da jama’arta masu kirki da kyawawan al’adunta da cimaka masu dadi, sabanin yadda kafafen watsa labarai na yammacin duniya ke gabatar da kasar Sin. Kana za su yi amfani da fasahohin zamani wajen watsa abubuwan da suka gani ga ’yan uwansu da sauran jama’ar duniya, lamarin da zai kara wayar da kan duniya game da yanayin da duniya take ciki da kuma bayyana gaskiya a zahirance.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Karya fure take ba ta ’ya’ya! Baki daga kasashen duniya daban daban na da damar ziyartar wurare daban daban na kasar Sin tare da mu’amala da Sinawa da ganin al’adun da ci gaban kasar a zahiri, lamarin da zai ba su damar gina ra’ayi ko tunanin na kashin kansu game da kasar Sin, wanda babu wanda zai iya sauyawa ko gogewa, kana za su iya fayyace gaskiya da karya don gane da karairayin da suka dade suna ji.

 

Har kullum kasar Sin kan ce ba ta da abun boyewa, kofarta a bude take domin jama’ar duniya su kawo ziyara don ganin wannan kyakkyawan kasa mai tafiya da zamani, dake samun ci gaba a kullum, wadda kuma ke da abubuwa masu ban sha’awa ga duk wanda ya ziyarce ta. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Philippines Ta Zamo Mai Tada Zaune Tsaye A Yankin Tekun Kudancin Sin

Next Post

NLC Ta Bukaci A Dage Sauraron Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Shugabanta Zuwa 29 ga Agusta 

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

6 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

6 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

8 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

9 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

17 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

18 hours ago
Next Post
NLC

NLC Ta Bukaci A Dage Sauraron Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Shugabanta Zuwa 29 ga Agusta 

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.