Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya gargaɗi gwamnatin tarayya cewa, kada a yi sakaci Birai da Macizai su Haɗiye dala biliyan 1.07 da aka ware wa fannin lafiya a kasafin kudin 2025.
Atiku a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ya bukaci a samar da hanyoyin da za a tabbatar da an yi amfani da kudaden wajen inganta harkokin kiwon lafiya maimakon karkatar da su, ta yadda za su zama cikin lalube.
- Ba Laifi A Binciki Gwamnatin Mahaifina, Amma A Yi Da Zuciya Ɗaya – Bello El-Rufai
- Gwamna Zulum Ya Mika Sandar Mulki Ga Sabon Shehun Dikwa
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya yi nuni da cewa, bai kamata a ce dabbobi irin su Macizai da Birai ne ke da alhakin bacewar kudaden jama’a ba, bai kamata irin haka ta faru a kudaden kasafin kiwon lafiya ba.
Ya kuma yi kira da a samar da tsari na gaskiya da rikon amana don bin diddigin yadda ake kashe kudaden da aka ware domin amfanin jama’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp