• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta bayyana cewa ɓangaren noma zai samu kaso 6.21 cikin 100 na kasafin Kuɗin shekarar 2024 da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya gabatar a gaban zauren Majalisar dokokin jihar Katsina.

Kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Katsina, Alhaji Bello Kagara ya bayyana haka ga manema labarai a Katsina.

  • Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnati
  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Kwamishinan ya ce, gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya tabbatar da kasafin kudin shekarar 2024 na Naira biliyan 454,308,862,113.96 amma ɓangaren ya samu naira biliyan 20, 513,909,753.71 inda haka ke nuna ya samu kaso 6.21%.

Haka kuma ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka da ake sa ran zasu lakume biliyoyin nairori a cikin kasafin shekarar 2024 da suka haɗa da ɓangaren Ruwan Sha da Ilimi da Kiwon lafiya da Ayyuka da Muhalli sai kuma noma.

” Bangaren ruwan sha ana sa ran zai lakume kimanin naira biliyan 67,161,802,447.39 inda yake wakilcin kaso 20.35% sai kuma ɓangaren ilimi da zai lakume naira biliyan 66,422,889,400.21 shima yana wakilcin kaso 20.13%” inji shi

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Sauran ɓangarori sun haɗa da ma’aikatar ayyuka inda za a kashe kimanin naira biliyan 53,484,733,251.59 bisa wakilcin kaso 16.20% cikin ɗari, sai harkar kiwon lafiya ana sa ran zata kuɗi wuri na gugar wuri har naira biliyan 38,326, 421,172.23 cikin ɗari inda ta samu wakilcin kaso 11.43%.

Alhaji Bello Kagara ya cigaba da bayanin cewa ɓangaren muhalli zai samo naira biliyan 37,700,909,753.24 kaso 11.43% cikin ɗari wanda jumlar kuɗin suka kasance Naira biliyan 282,607,873,235.37

Tunda farko da yake jawabin sa Kwamishinan ya ce kasafin Kuɗin wannan shekarar na 2024 ya ɗararwa na bara da kimanin biliyan 153,675,604,150.96 daidai da kaso 51.11%

Kazalika Alhaji Bello Kagara ya ce wannan kasafin kudi na shekarar 2024 mai taken ‘Gina Gobe’ za a aiwatar da shi da waɗannan hanyoyin kuɗaɗen shiga.

A cewar Kwamishinan ana sa ran samun kuɗaɗen shiga daga hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta jihar Katsina da ma’aikatu da hukumomin gwamnati inda ake sa ran samun kimanin naira biliyan 25,826,650,462.67 sai kuma kuɗaɗen da wasu hukumomin gwamnati za su samar da suka kai kimanin naira biliyan 14,173,349,537.33

Sai kuma ya kara da cewa akwai kuɗaɗen da ake sa ran samu daga ɓangaren rabon arzikin ƙasa kimanin naira biliyan 148,061,977,186.28 da sauran ɓangarori na kuɗaɗen shiga.

Wannan kasafin kudi na shekarar 2024 bangaren ayyukan yau da kullum zai lashe kimanin naira biliyan 124,329,343,517.99 sai kuma manyan ayyuka za su kashi naira biliyan 329,979,518,595.97 jumla naira biliyan 454,308,862,113.96.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwaman KatsinaKasafin kudin jihar KatsinaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ribar Masana’antun Sin Ta Karu A Watan Oktoba

Next Post

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa ‘Yan Jarida ‘Yanci

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

9 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

10 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

11 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

12 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

13 hours ago
Next Post
Amurka

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa 'Yan Jarida 'Yanci

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.