ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Noma

Gwamnatin jihar Katsina ta bayyana cewa ɓangaren noma zai samu kaso 6.21 cikin 100 na kasafin Kuɗin shekarar 2024 da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya gabatar a gaban zauren Majalisar dokokin jihar Katsina.

Kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Katsina, Alhaji Bello Kagara ya bayyana haka ga manema labarai a Katsina.

  • Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnati
  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Kwamishinan ya ce, gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya tabbatar da kasafin kudin shekarar 2024 na Naira biliyan 454,308,862,113.96 amma ɓangaren ya samu naira biliyan 20, 513,909,753.71 inda haka ke nuna ya samu kaso 6.21%.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka da ake sa ran zasu lakume biliyoyin nairori a cikin kasafin shekarar 2024 da suka haɗa da ɓangaren Ruwan Sha da Ilimi da Kiwon lafiya da Ayyuka da Muhalli sai kuma noma.

” Bangaren ruwan sha ana sa ran zai lakume kimanin naira biliyan 67,161,802,447.39 inda yake wakilcin kaso 20.35% sai kuma ɓangaren ilimi da zai lakume naira biliyan 66,422,889,400.21 shima yana wakilcin kaso 20.13%” inji shi

LABARAI MASU NASABA

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sauran ɓangarori sun haɗa da ma’aikatar ayyuka inda za a kashe kimanin naira biliyan 53,484,733,251.59 bisa wakilcin kaso 16.20% cikin ɗari, sai harkar kiwon lafiya ana sa ran zata kuɗi wuri na gugar wuri har naira biliyan 38,326, 421,172.23 cikin ɗari inda ta samu wakilcin kaso 11.43%.

Alhaji Bello Kagara ya cigaba da bayanin cewa ɓangaren muhalli zai samo naira biliyan 37,700,909,753.24 kaso 11.43% cikin ɗari wanda jumlar kuɗin suka kasance Naira biliyan 282,607,873,235.37

Tunda farko da yake jawabin sa Kwamishinan ya ce kasafin Kuɗin wannan shekarar na 2024 ya ɗararwa na bara da kimanin biliyan 153,675,604,150.96 daidai da kaso 51.11%

Kazalika Alhaji Bello Kagara ya ce wannan kasafin kudi na shekarar 2024 mai taken ‘Gina Gobe’ za a aiwatar da shi da waɗannan hanyoyin kuɗaɗen shiga.

A cewar Kwamishinan ana sa ran samun kuɗaɗen shiga daga hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta jihar Katsina da ma’aikatu da hukumomin gwamnati inda ake sa ran samun kimanin naira biliyan 25,826,650,462.67 sai kuma kuɗaɗen da wasu hukumomin gwamnati za su samar da suka kai kimanin naira biliyan 14,173,349,537.33

Sai kuma ya kara da cewa akwai kuɗaɗen da ake sa ran samu daga ɓangaren rabon arzikin ƙasa kimanin naira biliyan 148,061,977,186.28 da sauran ɓangarori na kuɗaɗen shiga.

Wannan kasafin kudi na shekarar 2024 bangaren ayyukan yau da kullum zai lashe kimanin naira biliyan 124,329,343,517.99 sai kuma manyan ayyuka za su kashi naira biliyan 329,979,518,595.97 jumla naira biliyan 454,308,862,113.96.

Noma
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Next Post
Amurka

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa 'Yan Jarida 'Yanci

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.