ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin Kuɗin 2024: A Jihar Katsina, Ɓangaren Noma Zai Samu Kashi 6.21% Kawai – Kwamishina.

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Noma

Gwamnatin jihar Katsina ta bayyana cewa ɓangaren noma zai samu kaso 6.21 cikin 100 na kasafin Kuɗin shekarar 2024 da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya gabatar a gaban zauren Majalisar dokokin jihar Katsina.

Kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Katsina, Alhaji Bello Kagara ya bayyana haka ga manema labarai a Katsina.

  • Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Shugaban Ma’aikatan Gwamnati
  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas

Kwamishinan ya ce, gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya tabbatar da kasafin kudin shekarar 2024 na Naira biliyan 454,308,862,113.96 amma ɓangaren ya samu naira biliyan 20, 513,909,753.71 inda haka ke nuna ya samu kaso 6.21%.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka da ake sa ran zasu lakume biliyoyin nairori a cikin kasafin shekarar 2024 da suka haɗa da ɓangaren Ruwan Sha da Ilimi da Kiwon lafiya da Ayyuka da Muhalli sai kuma noma.

” Bangaren ruwan sha ana sa ran zai lakume kimanin naira biliyan 67,161,802,447.39 inda yake wakilcin kaso 20.35% sai kuma ɓangaren ilimi da zai lakume naira biliyan 66,422,889,400.21 shima yana wakilcin kaso 20.13%” inji shi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sauran ɓangarori sun haɗa da ma’aikatar ayyuka inda za a kashe kimanin naira biliyan 53,484,733,251.59 bisa wakilcin kaso 16.20% cikin ɗari, sai harkar kiwon lafiya ana sa ran zata kuɗi wuri na gugar wuri har naira biliyan 38,326, 421,172.23 cikin ɗari inda ta samu wakilcin kaso 11.43%.

Alhaji Bello Kagara ya cigaba da bayanin cewa ɓangaren muhalli zai samo naira biliyan 37,700,909,753.24 kaso 11.43% cikin ɗari wanda jumlar kuɗin suka kasance Naira biliyan 282,607,873,235.37

Tunda farko da yake jawabin sa Kwamishinan ya ce kasafin Kuɗin wannan shekarar na 2024 ya ɗararwa na bara da kimanin biliyan 153,675,604,150.96 daidai da kaso 51.11%

Kazalika Alhaji Bello Kagara ya ce wannan kasafin kudi na shekarar 2024 mai taken ‘Gina Gobe’ za a aiwatar da shi da waɗannan hanyoyin kuɗaɗen shiga.

A cewar Kwamishinan ana sa ran samun kuɗaɗen shiga daga hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta jihar Katsina da ma’aikatu da hukumomin gwamnati inda ake sa ran samun kimanin naira biliyan 25,826,650,462.67 sai kuma kuɗaɗen da wasu hukumomin gwamnati za su samar da suka kai kimanin naira biliyan 14,173,349,537.33

Sai kuma ya kara da cewa akwai kuɗaɗen da ake sa ran samu daga ɓangaren rabon arzikin ƙasa kimanin naira biliyan 148,061,977,186.28 da sauran ɓangarori na kuɗaɗen shiga.

Wannan kasafin kudi na shekarar 2024 bangaren ayyukan yau da kullum zai lashe kimanin naira biliyan 124,329,343,517.99 sai kuma manyan ayyuka za su kashi naira biliyan 329,979,518,595.97 jumla naira biliyan 454,308,862,113.96.

Noma
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Amurka

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa 'Yan Jarida 'Yanci

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.