• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

空撮 東京電力福島第一原発/処理水の海洋放出に向けて準備が進む東京電力福島第一原発=2023年7月4日午前10時52分、朝日新聞社ヘリから=福島県

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta ce bai kamata kasar Japan ta dauki rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) ta fitar a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba, tana mai bukatar Japan din ta hada hannu da hukumar IAEA wajen samar da wani tsarin sa ido na kasa da kasa, mai dogon zango.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan a lokacin da aka nemi ya yi tsokaci kan rahoton, wanda ya yi amana shirin Japan na zuba dagwalon nukiliya cikin teku ya dace da matakan aminci na kasa da kasa. Yana mai cewa, IAEA za ta dauki lokaci mai tsawo tana sa ido kan ayyukan Japan.
A cewar kakakin, an gano rahoton ya gaza bayyana cikakken ra’ayoyin masanan da suka nazarci shirin, haka kuma ba a sanar da dukkanin masanan sakamakon nazarin ba.

  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa Wajen Kare Mabanbantan Wayewar Kan Al’umma

Yana mai cewa, kasar Sin na takaicin gaggawar da aka yi wajen fitar da rahoton.
Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya maida martani kan rahoton hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA, na tantance aikin zubar da dagwalon ruwan nukiliyar kasar Japan cikin teku, inda ya jaddada cewa, bai kamata Japan ta dauki rahoton a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba.

Wang ya nuna cewa, rahoton ba ya shaida amincin shirin Japan, na juye dagwalon ruwan nukiliyar ta cikin teku, kana kuma, ba zai iya tabbatar da tsaron aikin ba. Jami’in ya jaddada cewa, juye dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, zai illata babbar moriyar kasa da kasa, don haka bai kamata a kuskure fahimtar hakan ba.

Game da batun, mai fashin baki yana mai cewa, bayan da ya duba rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA ya fitar jiya Talata 4 ga wata, wanda ya yi duba kan yunkurin kasar Japan na zubar da dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, babban jami’in kungiyar masu aikin su ta jihar Miyagi-ken ta kasar, Terazawa Haruhiko ya nuna damuwa sosai. Kamar yadda yake nuna damuwa kan hakan, jama’ar kasar Japan da dama suna ganin cewa, abun da rahoton ya bayyana, cewa wai shirin juye dagwalon ruwan nukiliya cikin teku na Japan, ya dace da ma’aunin tsaro na kasa da kasa, ba mai gamsarwa ba ne. Har ma kungiyoyin da ba na gwamnati ba da dama a kasar Koriya ta Kudu sun ce, bai dace rahoton ya zama dalilin Japan na juye dagwalon ruwan nukiliya cikin tekun ba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Saboda rahoton bai bayyana ra’ayoyin dukkan kwararrun da suka halarci aikin tantancewa ba, kuma sakamakon rahoton bai samu amincewa ta bai daya daga dukkan kwararrun ba.

Idan aka dubi ayyukan da kasar Japan take yi kwanan nan, akwai abubuwan shakku sosai a ciki. Mu dauki kasafin kudin hukumar farfado da kasar ta Japan na shekara ta 2021 a matsayin misali, kasafin kudin da ya shafi shawo kan tasirin hadarin makamashin nukiliya a tashar Fukushima ya karu zuwa kudin Japan Yen biliyan 2, wanda ya ninka har sau 4 idan aka kwatanta da na shekara ta 2020. Haka kuma, kafafen watsa labaran Koriya ta Kudu sun ce, kafin hukumar IAEA ta bullo da rahoton, gwamnatin Japan ta riga ta samu daftarin sa, har ma ta gabatar da ra’ayoyin gyaran shi.

Bugu da kari, an ce, jami’an gwamnatin Japan sun baiwa jami’an hukumar IAEA kyautar kudade da yawansu ya zarce EURO miliyan 1. Idan da gaske ne hakan, to, ina dalilin da ya sa gwamnatin Japan ta kashe wadannan kudade tare da yin irin wannan kokari?
Ba za’a iya amincewa da yunkurin gwamnatin Japan, na zubar da dagwalon ruwan nukiliya sama da ton miliyan 1 zuwa tekun Pasifik a cikin nan da shekaru 30 masu zuwa ba. Zabin Japan na zubar da shi kai-tsaye domin cimma muradun kanta, kawai haifar da hadari ne za ta yi, ga daukacin al’ummun duniya. (Masu Fassarawa: Fa’iza Mustapha, Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Shafe Shekara 14 Ba A Biya Tsofaffin Ma’aikata Fansho Da Kudin Sallama A Adamawa Ba

Next Post

Bayan Kin Gaskiya…

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

38 minutes ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

18 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

21 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

22 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
Bayan Kin Gaskiya…

Bayan Kin Gaskiya…

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.